Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
Published: 5th, July 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta bayyana a gun taron manema labarai da aka yi a yau Juma’a cewa, Sin na fatan kara hadin gwiwa da Ghana, don gaggauta bunkasuwar huldarsu ta abota bisa manyan tsare-tsare.
Yayin da Mao Ning take tsokaci game da cika shekaru 65 da kulla huldar diplomasiyya tsakaninsu, ta ce a ranar 5 ga watan nan da muke ciki, za a cika shekaru 65 da kalluwar huldar tsakanin kasashen biyu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran cin amanar diflomasiyya ce
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana harin da sojojin Amurka suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya a matsayin cin amanar diflomasiyya da kuma cewa wani mataki ne da ba a taba ganin irinsa ba ga tsarin doka da hakkin kasa da kasa da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da Ronald Lamola, ministan hulda da kasa da kasa da hadin gwiwa na Jamhuriyar Afirka ta Kudu, sun tattauna batutuwan baya-bayan nan da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya bayan dakatar da hare-haren soji da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka yi kan Iran a wata tattaunawa ta wayar tarho a ranar Laraba.
Araqchi ya bayyana jin dadinsa ga matsayin Afrika ta Kudu wajen yin Allah wadai da zaluncin sojin gwamnatin ‘yan sahayoniyya masu nuna wariyar al’umma suka dauka na kai wa kasar Iran hari, yana mai cewa: Hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta dauka a kan Iran, sakamakon rashin hukunta ta ce da kuma gazawar kasashen duniya wajen mayar da martani kan laifukan da take aikatawa a Gaza da kuma hare-haren da take kai wa Lebanon da Siriya, kuma tabbas dukkanin masu goya mata baya suna da hannu wajen aikata laifukan da take aikatawa.
Ya yi nuni da cewa: Harin da sojojin yahudawan sahayoniyya suka kai wa Iran ya faru ne a cikin shawarwari da kuma goyon bayan gami da taimakon Amurka. Daga nan ne Amurka ta kaddamar da harin soji kan cibiyoyin nukiliyar Iran na zaman lafiya, tare da jaddada cewa matakin da Amurka ta dauka ya zama cin amanar diflomasiyya da kuma wani matakin da ba a taba ganin irinsa ba na rashin bin doka da oda, da take hakkin kasa da kasa, da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya.