Limamin da ya jagoranci sallar Juma’a a birnin Tehra mya bayyana cewa: Hukuncin shari’a da ya hau kan Trumpm da Netanyahu shi ne kisa

Limamin da ya jagoranci sallar juma’a a birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran a yau ya bayyana cewa: Amurka da karen da suka horar sun yi barazana ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma wannan wauta ce.

Hakika dokar Musulunci ta Trump da Netanyahu ita ce mutuwa. Sun kashe mutane fiye da 55,000 a Gaza. Su suka kai Qasim Sulaimani da yin shahada da sauran abokansa. Su ne masu aiwatar da kisan kai da ayyukan fasadi a duniya. Sun yi wa Jagoran juyin juya halin Musulunci da al’ummar Iran barazana. Abin farin cikin shi ne, dukkanin hukumomin addini na birnin Qum da Najaf sun tashi tsaye tare da yin Allah wadai da wannan gurbatacciyar tunani. Sannan a baya-bayan nan Ayatullah Nasir Makarem Shirazi da Ayatullahi Nuri sun yi tofin Allah tsine kan wannan barazana da bayyana hakan a matsayin shelanta yaki.

Hujjatul-Islam Ahmad Khatami a cikin hudubar sallar juma’ar a birnin Tehran, yayin da yake ishara da harin da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta kai harin wuce gona da iri kan kasar Iran ya ce: martani da dakarun Iran suka mayar kan gwamnatin yahudawan sahayoniyya abu ne da ke gwada karfinsu na mayar da martini kan dukj wani mai girman kai da dagawa.

AYatullahi Hatami ya kara da cewa: Son kasa da kare Musulunci so ne ga Allah. Kuma kishin kasa wani bangare ne na Imani, don haka ya karfafa al’umma kan Shirin kare kasarsu da kimar daular Musulunci daga duk wani dan mamaya mai kiyayyaya da kyawawan dabi’un addini.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Janar Ali Fadli: IRGC Suna Da Damar Kera Makamin Nukiliya Da Kuma Rufe Mashigar Ruwan Hurmuz

Janar Ali Fadi wanda tashar talabijin din Iran ta yi hira da shi a jiya da dare, ya bayyana cewa; Iran tana da damar kera makamin Nukiliya da kuma rufe mashigar ruwan Hurzum.

Janar Fadli ya ce; Dakarun na kare juyin musulunci sun lakanci yadda ake kera shi, tare da bayyana fatan cewa kar  makiya su tafka  babban kuskuren da zai tura Iran yin tunanin hakan.”

Dangane da batun rufe mashigar ruwan Humuz kuwa, janar Faldi ya ce, suna da damar yin hakan,sai dai kuma ko kadan wannan ba ya cikin manufofin jamhuriyar musulunci.

Janar Fadli shi ne mai kula da tafiyar da ayyyuka a tsakanin bangarori daban-daban na dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Rattaba Hannu Kan Daftarin Dakatar Da
  • Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci
  •  A Yau Juma’a Ne Ake Gudanar Da Taron Karrama Shahid Birgediya Janar Husain Salami A Nan Birnin Tehran
  • Janar Ali Fadli: IRGC Suna Da Damar Kera Makamin Nukiliya Da Kuma Rufe Mashigar Ruwan Hurmuz
  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
  •  Muhsin Rizai: Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Bayar Da Umarni  Da Jagorantar Yakin “Wa’adussadiq 3”
  • Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
  • Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang