Yadda aka kashe dan fashi aka kama wasu 7 a Abuja
Published: 20th, May 2025 GMT
’Yan sanda sun bindiga wani wanda ake zargin dan fashi ne har lahira, sa’annan suka kwato bindigogi bakwai a unguwar Maitama da Abuja.
Kwamishinn ’Yan Sanda na Babban Birnin Tarayya, Ajoa Adewale, ya sanar a safiyar Talata, cewa rundunar ta kama gungun wasu mutum bakwai da suka kware wajen aikata fashi d makami da kuma kwcen motoci.
Ajao ya ce ’yan fashin suna ganin ’yan sanda suka bude musu wuta, inda jami’an suka yi nasarar harbe wani wanda aka fi sani da Baballe, har lahira, suka kama wasu guda bakwai. Shugaban ’yan fashin, wanda ake kira Pastor Mogu da wani mutum daya sun tsere da raunin harbi a jikinsu.
Abubuwan da aka kwace a hannun ’yan fashin sun hada da bindigogi kirar AK-47 guda hudu, pistol kirar gida guda biyu da wata babbar bindiga da harsasai. Sauran sun hada da mota kirar Toyota Corolla da kuma babur kirar Boxer.
Yadda DSS ta kama ɗan bindiga zai tafi aikin Hajji a Sakkwato An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a SaudiyyaKwamsihinan ’yan sandan ya ce mutum biyu daga cikin ’yan fashin, tsoffin fursunoni da wani wanda ’yan sanda suke nema bayan ya tsere daga inda ake tsare da shi a Jihar Bauchi.
Ya ce, an samu nasarar ne a wani samame da jami’an runduna ta musamman masu aikin ya ki da miyagun laifuka suka kaddamar.
Rundunar a cewarsa, ta dade tana hakon gungun ’yan fashin da suka addabi mutane da kwacen motoci.
Bayan samun rahoto shirinsu na fara aiki a unguwar Maitama ne jami’an rundunar suka shammace su.
Ajao ya ce ana ci gaba da bincike kuma da zarar an kammala za a gurfanar da su a gaban kuliya domin su fuskanci hukunci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan fashi kwacen motoci
এছাড়াও পড়ুন:
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato
Aƙalla mutane bakwai sun mutu yayin da wasu 11 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya faru a ƙauyen Essa da ke kan hanyar Agaie-Badeggi, ƙaramar hukumar Katcha, jihar Neja.
Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa motar ɗauke da hatsi ta gwamnatin tarayya ce, kuma fasinjojinta maza ne kimanin 36, daga Legas zuwa Kano.
Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato An Tsinci Gawarwakin Yara Biyar Cikin Tsohuwar Mota A NasarawaHatsarin ya faru ne da ƙarfe 3 na daren ranar Lahadi, lokacin da direban ya yi ƙoƙarin ƙetare wani ɓangare mara kyau na hanyar da ake ginawa.
Daraktan hukumar kula da sufuri na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana kan aikin ceto da binciken kan iftila’in.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp