Rundunar sojin Najeriya ta ce za ta fara atisayen tantance gwanintar harbi na shekarar 2025 daga ranar Litinin 17 zuwa 19 ga watan Maris a Barikin Yar Gaba da ke Dutse, Jihar Jigawa.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 26 Armoured Brigade, Laftanar Uzoma Egwu-Ukpai, ya sanyawa hannu aka kuma bai wa gidan rediyon Najeriya a Dutse.

Sanarwar ta bayyana cewa, atisayen tantance gwanintar harbi ana yi ne domin auna ƙwarewar jami’an soji wajen sarrafa makamai da ingancin harbinsu.

Laftanar Uzoma Ukpai ya shawarci al’umma da kada su firgita yayin atisayen idan suka ga sojoji suna kai-komo ko suka ji karar harbi, musamman mutanen da ke zaune a yankin Yargaba.

Haka kuma, Mataimakin Daraktan ya umarci manoma da mafarauta da ke kusa da wurin atisayen da su guji yankunansu na noma da farauta a lokacin atisayen.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Harbi Jigawa Rundunar Soji

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

An haife ni a a ‘Delta state’, na yi makarantar firamare da sakandare a Delta, sannan nayi aure a can. Yara na uku, Allah ya kawo rabuwa tsakani na da mijina. Babana dan ‘Nasarawa State’ ne, Mama ta kuma ‘yar Jihar Kano ce. Shekaruna Talatin da hudu, na tsinci kaina a masana’antar Kannywood ne shekara shida da suka wuce baya.

 

Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood?

Saboda fim yana daya daga cikin abin da ya fara burge ni bayan aure na ya mutu, shi fim abu ne wanda yake kamar wa’azantarwa da kuma tunatarwa.

 

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?

Yadda gwagwarmayar ya kasace shi ne; na zo fim ne ba tare da tunanin yadda za ta kasance da ni ba, amma yanzu kam Alhamdulillah.

 

Ya batun iyaye lokacin da za ki sanar musu kina sha’awar fara fim, shin kin samu wani kalubale daga gare su?

Eh, a gaskiya na samu. Saboda mahaifiya ta da ‘yan’uwana sun ki yarda, sai da na samu na zaunar da su na fahimtar da su sannan.

 

Da wane fim ki ka fara?

‘Motsin Rai’ wanda Yahaya Sa’id ne yayi daraktin, da kuma Dadin Kowa.

 

Ya farkon farawar ta kasance?

Gaskiya na sha wahala kasancewar shi ne farkon dasa min ‘camera’.

 

Da su wa ki ka fara cin karo a farkon shigarki kannywood?

Bosho, su Dan’Auta da sauransu.

 

Kin yi finafinai sun kai kamar guda nawa?

Gaskiya ba zan iya kirgawa ba.

 

Cikin finafinan da ki ka fito wanne ne ya zamo bakandamiyyarki?

Kishiyar uwa, saboda na fito a mahaukaciya abun dai abun armashi.

 

Wane irin nasarori ki ka samu game da fim?

Dalilin fim na je gurare wanda ban da ta wannan hanya, ban yi tunanin zuwa ba.

 

Ko akwai wani kalubale da ki ka taba fuskanta cikin masana’antar?

Eh, kam ba za a rasa ba, to, amma Alhamdulillah.

 

Wane abu ne ya taba faruwa da ke na farinciki ko akasin haka, wanda ba za ki taba iya mantawa da shi ba a rayuwa?

Kamar mutuwar mahaifi na, ba zan taba iya mantawa ba har abada.

 

Ko kina da ubangida a masana’anyar Kannywood?

Eh, ina da shi.

 

Kafin shigarki masana’antar Kannywood wadanne jarumai ne suke burge ki, kuma me ya sa?

Ali nuhu, saboda yadda yake aikinsa kamar a gaske.

 

Mene ne burinki na gaba game da fim?

In zama babbar jaruma.

 

Bayan fim kina wata sana’ar ne?

Eh, ina ‘business’.

 

Misali wani daga cikin abokan aikinki ya ce yana sonki zai aure ki, shin za ki amince ki aure shi ko kuwa ba ki da ra’ayin auren dan fim?

Idan da so da kauna me zai hana.

 

Wasu na kokawa game da masana’antar kannywood, a takaice ya za ki yi wa masu karatu bayanin yadda masana’antar take, shin wace ce Kannywood ya cikinta yake?

Kannywood wata masana’anta ce wacce take kamar makaranta, kafin ka fara ta, dole sai ka mayar da hankali.

 

Wane kira za ki yi ga masu kokarin shiga kannywood?

Duk wacce za ta shigo ta dauka kamar koyan sana’a ce ya kawo ta, dole sai ta mayar da hankali tare da jajircewa.

 

Ko akwai wata shawara ko wani sako da ki ke da shi ga sauran abokan aikinki?

Sako na a gare su shi ne, su dinga rike gaskiya da amana, su sani mu kamar amana muke a hannunsu, su taya mu rike ta kima da mutuncin mu.

 

Me za ki ce da masoyanki masu kallon finafinanki?

Ina yi wa kowa fatan alkairi.

Muna godiya

Ni ma na gode.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gwarzon Mawaƙin Shekarar 2025, Skales October 25, 2025 Nishadi Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad  October 11, 2025 Nishadi Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri? October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu