Aminiya:
2025-05-20@20:41:14 GMT

Zulum zai saya wa sojoji da ’yan sa-kai ƙarin motoci don yaƙar Boko Haram

Published: 20th, May 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya amince da sayen ƙarin motoci guda 10 don taimaka wa sojoji da ’yan sa-kai wajen yaƙi da ’yan Boko Haram da ISWAP.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wata ziyara da ya kai Kala-Balge, inda ya gana da ƙungiyoyi daban-daban.

An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato Yadda ’yan sanda suka kashe dan fashi suka kwato bindigogi 7 a Abuja

Ya ce za a bai wa ’yan sa-kai motoci shida ƙirar Toyota Hilux, ciki har da CJTF, mafarauta da ’yan banga, sannan za a bai wa sojoji ƙarin motoci huɗu masu bindiga.

Zulum, ya kuma raba wa iyalai 10,000 da ke fama da talauci a yankin kayan abinci, yawancin waɗanda suka samu kayan mata da marasa galihu ne.

A garin Rann, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Kala-Balge, gwamnan ya kwana a can tare da duba lafiyar jami’an tsaro da kuma tallafa musu.

Zulum, ya ce ziyarar tana cikin ƙoƙarinsa na ƙarfafa haɗin kai da juriya a tsakanin al’ummar jihar, duba da ƙalubalen tsaro da suke fuskanta daga ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP.

Ya ce, “Ina kira ga dukkanin mazauna Borno da su haɗa kai da jami’an tsaro domin kare mu daga barazanar tsaro.”

Zulum, ya kuma nuna godiyarsa ga al’ummar jihar da sauran yankuna da suka amsa kiran yin azumi da addu’a domin samun zaman lafiya.

Ya ce mutane daga wasu jihohi da ma ƙasashen waje sun haɗa kai da su wajen neman taimakon Allah domin kawo ƙarshen matsalar tsaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan sa Kai Boko Haram yaƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Senegal ta karbi wani sansaninta na uku daga hannun Faransa

Kasar Faransa ta mika iko na sansanin soja na Contre-Amiral Protet ga kasar Senegel, wanda shi ne sansanin soja na 3 da aka mikawa kasar a bana.

An mika sauran sansanoni biyu da suka hada da Marechal da Sanit-Exupery ne a watan Maris din da ya gabata, Kuma dukkan sansanonin na da mazauni ne a Dakar, babban birnin Senegal.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin Faransa ya fitar, ta ce an tsara mika dukkan wasu sansanonin dake karkarshin ikon Faransa a Senegal a bana, biyo bayan yarjejeniyar da kasashen biyu suka yi.

A ranar 31 ga watan Disamban 2024, shugaban Senegal Bassirou Diomaye Faye ya sanar a jawabinsa na sabuwar shekara cewa, za a bukaci dakarun Faransa su fara janyewa daga kasar a bana.

A shekarun baya bayan nan dai kasashen Afrika sun yi ta kira da janye dakarun Faransa daga kasashensu.

Shi ma a jawabinsa na sabuwar shekara, shugaban Ivory Coast Alassane Ouattara, ya gabatar da shirin ficewar dakarun Faransa daga kasarsa.

Tun tuni daga kasashen Mali, Burkina Faso da Nijar suka raba gari da kasar ta Faransa tare da yanke alakar soji a tsakaninsu, sai kuma kasar Chadi wacce ta bi sahu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato
  • NiDCOM Ta Ceto ‘Yan Nijeriya 13 Da Aka Yi Safarar Zuwa Ghana Da Mali
  • An cimma matsaya kan dakatar da haska fina-finai 22 a Kano
  • Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki
  • Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5
  • Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
  • An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja
  • Senegal ta karbi wani sansaninta na uku daga hannun Faransa
  • Guguwar raba Masarautar Katsina ta kunno kai