Zulum zai saya wa sojoji da ’yan sa-kai ƙarin motoci don yaƙar Boko Haram
Published: 20th, May 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya amince da sayen ƙarin motoci guda 10 don taimaka wa sojoji da ’yan sa-kai wajen yaƙi da ’yan Boko Haram da ISWAP.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wata ziyara da ya kai Kala-Balge, inda ya gana da ƙungiyoyi daban-daban.
An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato Yadda ’yan sanda suka kashe dan fashi suka kwato bindigogi 7 a AbujaYa ce za a bai wa ’yan sa-kai motoci shida ƙirar Toyota Hilux, ciki har da CJTF, mafarauta da ’yan banga, sannan za a bai wa sojoji ƙarin motoci huɗu masu bindiga.
Zulum, ya kuma raba wa iyalai 10,000 da ke fama da talauci a yankin kayan abinci, yawancin waɗanda suka samu kayan mata da marasa galihu ne.
A garin Rann, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Kala-Balge, gwamnan ya kwana a can tare da duba lafiyar jami’an tsaro da kuma tallafa musu.
Zulum, ya ce ziyarar tana cikin ƙoƙarinsa na ƙarfafa haɗin kai da juriya a tsakanin al’ummar jihar, duba da ƙalubalen tsaro da suke fuskanta daga ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP.
Ya ce, “Ina kira ga dukkanin mazauna Borno da su haɗa kai da jami’an tsaro domin kare mu daga barazanar tsaro.”
Zulum, ya kuma nuna godiyarsa ga al’ummar jihar da sauran yankuna da suka amsa kiran yin azumi da addu’a domin samun zaman lafiya.
Ya ce mutane daga wasu jihohi da ma ƙasashen waje sun haɗa kai da su wajen neman taimakon Allah domin kawo ƙarshen matsalar tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan sa Kai Boko Haram yaƙi
এছাড়াও পড়ুন:
Lakurawa sun kashe mutane 15 a Sakkwato
Wasu ‘yan bindigar da ake zargi Lakurawa ne sun kashe mutane sama da 15 a wani sabon hari a Karamar Hukumar Tangaza ta Jihar Sakkwato.
Wani mazauni kauyen Kwalajiya ya ce ‘yan bindigar Lakurawa sun zo kauyen a daren Lahadi har zuwa Asuba ta ranar Litinin inda suka kashe wasu mutane, a yayin da suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi.
“Bayan sun kashe mana mutane sun tafi da dabbobi masu yawa, duk da mutanenmu sun yi kokari amma yawan maharan da makaman da suke dauke da su ya sa suka fi karfinmu.
“Har zuwa yanzu ba mu san adadin wadanda aka kai asibiti ba domin suna da yawa, sai dai wadanda suka rasu 15 muka yi wa Sallah.
“Muna kira ga jami’an tsaro su mayar da hankali wurin korar mana wadannan ‘yan bindigar don mu samu zaman lafiya a jiha baki daya.”
Babban Jami’in Kungiyar Agaji Red Cross a Sakkwato, Alhaji Abubakar Ainu ya ce harin ya matukar tayar da hankalin mutanen yankin saboda an dauki dogon rabon da a samu irin hakan.
Ainu ya ce, “jami’anmu sun ziyarci kauyen Kwalajiya da ke Mazabar Magoho a garin Tangaza domin jajantawa da kuma halartar Sallar Jana’izar mutanen da ‘yan bindigar suka kashe sama da 15.
“Waxanda suka jikkata an kai su Asibitin Kashi na Wamakko da Asibitin Koyarwa ta Jam’ar Usmanu Danfodiyo da na Kwararru a birnin Sakkwo domin karbar magani.”
Ya ce yankin na cikin wuraren da ke fama da matsalar barayin shanu da masu tayar da kayar baya.
“Wannan lamari ba ya da dadi ko kadan, dubi yadda aka mayar da wasu mata zawarawa aka mayar da wasu yara marayu domin biyan wata bukata wadda addini bai yarda da ita ba. Ina kira ga hukuma ta sake salon yakar ‘yan bindiga da take yi,” in ji Ainu.