Aminiya:
2025-05-20@21:03:25 GMT

’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano

Published: 20th, May 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama wasu mutum shida da ake zargi da aikata fashi da makami tare da ƙwato motocin sata guda huɗu, bayan wani samame da suka kai.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce sun samu nasarar ne a ranar 10 ga watan Mayu, 2025, inda tawaga ta musamman ƙarƙashin jagorancin CSP Rabiu Gidado ta kama wani da ake zargi, Saidu Abubakar, a Jihar Filato.

Malamai sun gindaya sharaɗi kafin janye yajin aiki a Abuja  An kama ɗan bindiga a hanyar zuwa aikin Hajji a Sakkwato

An same shi da wata mota ƙirar Toyota Corolla samfurin 2016 da aka sace wa wani mazaunin unguwar Naibawa a Kano.

Yayin gudanar da bincike, Abubakar ya amsa cewa yana cikin wata ƙungiyar masu satar motoci da fashi da makami, kuma ya bayyana yadda suke aiwatar da ta’asarsu.

Kiyawa, ya kuma ce a ranar 16 ga watan Mayu, jami’an rundunar sun kama wani Ibrahim Isa a Kano, yana ƙoƙarin sayar da wata mota ƙirar Howo concrete mixer da aka sace a Ƙaramar Hukumar Kazaure a Jihar Jigawa.

Kakakin ya ce dukkanin waɗanda ake zargin na taimaka wa bincike, kuma za a gurfanar da su a kotu da zarar an kammala bincike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan fashi Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe ’yan kasuwa 15 a wani sabon hari a Binuwai

Aƙalla ’yan kasuwa 15 ne aka kashe a wani sabon hari da wasu ‘yan bindiga suka kai wasu garuruwa da ke Ƙaramar Hukumar Agatu a Jihar Binuwai.

’Yan kasuwar na kan hanyarsu ta komawa gida daga kasuwar Oweto da yammacin ranar Asabar lokacin da aka kai musu hari a kusa da garuruwan Ogwumogbo da Okpo’okpolo.

An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa

Tsohon mataimakin shugaban Ƙaramar Hukumar Agatu, John Ikwulono, ya tabbatar da faruwar harin, inda ya ce mutane da dama sun jikkata.

Ya ce mutum biyar aka kashe a kusa da wani ƙaramin rafin da ake kira Abekoko.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Agatu na yanzu, Melvin James, yana wajen jana’izar waɗanda aka kashe lokacin da manema labarai suka kira shi.

Hadiminsa ne, ya ɗauki waya, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ɗora laifin kan makiyaya masu ɗauke da makamai.

Da aka tuntuɓi sakataren Ƙungiyar Miyetti Allah na jihar, Ibrahim Galma, ya ce bai da masaniya game d harin ba amma zai bincika.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, bai yi wani ƙarin haske ba.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, CSP Catherine Anene, ta ce har yanzu ba ta samu rahoton harin ba.

Wannan hari ya ƙara yawan mutanen da aka kashe a Jihar Binuwai daga ranar 1 ga watan Afrilu zuwa 17 ga watan Mayu zuwa 174.

Sai dai mazauna yankin sun ce adadin na iya wuce haka, duba da yadda wasu hare-hare ba a kai rahotonsu ba ga hukumomin tsaro.

Yankuna da dama a jihar sun fuskanci hare-hare a baya-bayan nan, ciki har da Gwer ta Gabas, Guma, yankin Sankera (Katsina-Ala, Logo, Ukum), Otukpo, Gwer ta Yamma, Kwande, Apa, Agatu da Makurdi.

Yankin Sankera ne ya fi fuskantar hare-hare, inda aka kashe aƙalla mutum 83 tsakanin 17 zuwa 21 ga watan Afrilu kaɗai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati za ta sayar da gidaje 753 da EFCC ta ƙwato a hannun Emefiele 
  • ‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja
  • Yadda aka kashe dan fashi aka kama wasu 7 a Abuja
  • DSS Ta Cafke Ɗan Bindiga Yayin Da Yake Shirin Tafiya Aikin Hajji A Sakkwato 
  • ’Yansanda Sun Kama Wani Mutum Sanye Da Kayan Mata A Coci A Adamawa
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wani Kasurgumin Barowon Shanu Da Garkuwa Da Mutane A Kasuwar Shinge
  • Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Tsaro
  • An kashe ’yan kasuwa 15 a wani sabon hari a Binuwai
  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa