‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja
Published: 20th, May 2025 GMT
Bayan haka, ‘yansanda sun hanzarta daƙile harin, inda suka kama su a ranar 15 ga watan Mayu, 2025.
Da ‘yan fashin suka hango ‘yansanda, sai suka fara harbi.
A lokacin musayar wutar ne, Babanle ya mutu.
‘Yansanda sun kama sauran tawagar ƙungiyar guda bakwai a wajen.
Wasu daga cikinsu tsoffin fursunoni ne, yayin da ɗaya daga cikinsu fursuna ne da ya tsere daga gidan yari.
Hakazalika, ‘yansanda sun ƙwato wasu kayayyaki ciki har da mota ƙirar Toyota Camry, babur ƙirar boxer, harsasai, bindigogi ƙirar AK-47 da kuma wata bindiga ƙirar gida.
SP Adeh, ta ƙara da cewa shugaban ƙungiyar, Solomon Bawa wanda aka fi sani da Fasto Mogu, ya tsere tare da wani mutum bayan sun samu rauni.
Ta roƙi jama’a da su sanar da ‘yansanda idan sun ga wani da raunin harbin bindiga.
Ta ce duk waɗanda aka kama suna hannun ‘yansanda, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yansanda Ɗan Fashi yansanda sun
এছাড়াও পড়ুন:
Abba ya naɗa Ahmed Musa a matsayin Babban Manajan Kano Pillars
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sauya shugabancin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars.
Ya naɗa tsohon kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa, a matsayin sabon Babban Manajan ƙungiyar.
An gano wasu bama-bamai 56 da ISWAP suka binne a Borno “ADC za ta fuskanci matsala wajen zaɓen wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa”Wannan mataki na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na sake gina ƙungiyar kafin tunkarar kakar wasa ta 2025-2026 a Gasar Firimiyar Najeriya (NPFL).
A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Juma’a, an yanke hukuncin ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a harkar kwallon ƙafa.
Gwamnatin ta rushe tawagar hukumar wasanni ta jihar tare da naɗa wasu sabbi, wadda ke da mambobi 17; Ali Muhammad Umar (Nayara) ne jagorance ta.
Sauran mambobin sun haɗa da Salisu Mohammed Kosawa, Yusuf Danladi (Andy Cole), Idris Malikawa Garu, Nasiru Bello, Muhammad Ibrahim (Hassan West), Hamza Abdulkarim Audi Chara.
Akwai Muhammad Danjuma Gwarzo, Mustapha Usman Darma, Umar Dankura, Ahmad Musbahu, Gambo Salisu Shuaibu Kura, Rabiu Abdullahi, Aminu Ma’alesh da Safiyanu Abdu.
Abubakar Isah Dandago Yamalash ya ci gaba da zama Daraktan Harkokin Watsa Labarai, sannan Ismail Abba Tangalash ya ci gaba da riƙe matsayin Daraktan Labarai na II.
A wani muhimmin mataki, hukumar ta zaɓi Ahmed Musa a matsayin sabon Babban Manajan ƙungiyar.
Ahmed Musa, wanda ya taɓa buga wa Kano Pillars wasanni kuma ya taka rawar gani a duniya, ana sa ran zai kawo sauyi, tsari da kuma ɗaukaka ƙungiyar.
Gwamna Abba, ya bayyana cewa yana da yaƙinin sabuwae tawagar hukumar za ta ci gaba da samo nasarori.
“Naɗin Ahmed Musa na nuna yadda muke ƙoƙarin samar da ƙwarewa da gogewa a harkar ƙwallon kafa.
“Muna da yaƙinin cewa kasancewarsa a ƙungiyar zai ƙara wa ‘yan wasa ƙwarin gwiwa, ya ja hankalin masu zuba jari, sannan ya faranta ran magoya baya,” inji sanarwar.
Kano Pillars, na ɗaya daga cikin fitattun ƙungiyoyin kwallon kafa a Najeriya, ana sa ran za a samu sauye-sauye ƙarƙashin sabon shugabancin.