Aminiya:
2025-11-02@06:07:20 GMT

An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato

Published: 20th, May 2025 GMT

Wasu makiyaya biyu sun rasu bayan da wasu da ba a san ko su wane ne ba suka buɗe musu wuta a kusa da ƙauyen Tahore, da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos, a Jihar Filato.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da mamatan ke dawowa daga kasuwar Maikatako a kan babur.

Yadda ’yan sanda suka kashe dan fashi suka kwato bindigogi 7 a Abuja Harin ’yan bindiga ya sa Zamfarawa sun koma kwana a jeji

Shugaban Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah a Jihar Filato, Ibrahim Yusuf Babayo, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana sunan mamatan a matsayin Umar Sa’idu da Rashida Yakubu.

Ya ce lamarin ya faru ne da yamma, kuma ya sanar da manyan jami’an tsaro ciki har da sojoji da ’yan sanda.

Babayo ya yi Allah-wadai da kisan, ya kuma roƙi hukumomin tsaro da su ɗauki mataki don hana sake faruwar irin haka a gaba.

Ya kuma buƙaci ’yan uwansa Fulani da su kwantar da hankalinsu tare da kaucewa ɗaukar doka a hannu.

“Abin da ke faruwa da al’ummarmu yana da matuƙar tayar da hankali. Mun riga mun rasa shanu sama da ɗari tare da wasu makiyaya. Yanzu kuma an kashe mana wasu biyu,” in ji shi.

Sai dai wani jigo a ƙungiyar raya al’adu ta Bokkos (BCDC), John Apollos Maton, ya ce bai da labarin faruwar harin.

Ya kuma musanta cewa mutanensu na da hannu a lamarin, inda ya bayyana cewa su dai kawai suna kare kansun ne daga ’yan ta’adda.

Mai magana da yawun Rundunar Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, bai amsa tambayar da wakilinmu ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Tun da farko, Aminiya ta ruwaito cewa an kai hare-hare da dama ƙauyukan Bokkos tsakanin watan Maris da Afrilu, inda mutane da dama suka mutu.

Hukumomin tsaro sun tura jami’ansu domin wanzar da da zaman lafiya a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare Makiyaya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi

Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da fasinjoji a cikin wasu motocin bas Toyota guda biyu a titin Itobe zuwa Ajegwu-Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu ta jihar Kogi.

An samu rahoton cewa, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 5 na asubahi a tsakanin ƙauyukan Ojiwo’-Ajengo da Mamereboh da ke kan babbar hanyar.

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa

An ce masu garkuwa da mutanen sun yi amfani da wata tirela da aka kama wajen tare hanyar bayan shingen binciken jami’an tsaro, da ke kusa da wurin da lamarin ya faru.

Shedun gani da ido sun ce ɗaya daga cikin motocin bas ɗin mai lamba KG: KPA 622LG na kan hanyarta zuwa Abuja, tare da fasinjoji daga wata tashar mota a unguwar Ankpa da ke yankin Kogi ta Gabas.

Har yanzu ba a iya gano adadin fasinjojin da aka yi garkuwa da su ba zuwa yanzu, sai dai mun iya tabbatar da cewa ɗaya daga cikin motocin na ɗauke da fasinjoji ne daga yankin Ankpa, kamar yadda aka gano wasu takardu da wasu kayayyaki a wurin da lamarin ya faru suka bayyana.

“Motocin bas ɗin guda biyu suna kan hanyar Abuja ne a lokacin da suka ci karo da shingayen ’yan bindiga a safiyar ranar Alhamis. Dukkanin fasinjojin, ciki har da direban motocin bas ɗin biyu an yi awon gaba da su cikin daji,” in ji Unubi Ademu, wani mazaunin Achigili, a ƙauyen da ke maƙwabta.

Al’ummar yankin sun ƙara da cewa, jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji da mafarauta da kuma ’yan banga suna ƙoƙarin magance lamarin.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Kogi (PPRO), CSP William Aya bai amsa kira da saƙo ba lokacin da aka tuntuɓe shi har zuwa lokacin tattatara wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati