Aminiya:
2025-05-20@17:43:37 GMT

An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato

Published: 20th, May 2025 GMT

Wasu makiyaya biyu sun rasu bayan da wasu da ba a san ko su wane ne ba suka buɗe musu wuta a kusa da ƙauyen Tahore, da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos, a Jihar Filato.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da mamatan ke dawowa daga kasuwar Maikatako a kan babur.

Yadda ’yan sanda suka kashe dan fashi suka kwato bindigogi 7 a Abuja Harin ’yan bindiga ya sa Zamfarawa sun koma kwana a jeji

Shugaban Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah a Jihar Filato, Ibrahim Yusuf Babayo, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana sunan mamatan a matsayin Umar Sa’idu da Rashida Yakubu.

Ya ce lamarin ya faru ne da yamma, kuma ya sanar da manyan jami’an tsaro ciki har da sojoji da ’yan sanda.

Babayo ya yi Allah-wadai da kisan, ya kuma roƙi hukumomin tsaro da su ɗauki mataki don hana sake faruwar irin haka a gaba.

Ya kuma buƙaci ’yan uwansa Fulani da su kwantar da hankalinsu tare da kaucewa ɗaukar doka a hannu.

“Abin da ke faruwa da al’ummarmu yana da matuƙar tayar da hankali. Mun riga mun rasa shanu sama da ɗari tare da wasu makiyaya. Yanzu kuma an kashe mana wasu biyu,” in ji shi.

Sai dai wani jigo a ƙungiyar raya al’adu ta Bokkos (BCDC), John Apollos Maton, ya ce bai da labarin faruwar harin.

Ya kuma musanta cewa mutanensu na da hannu a lamarin, inda ya bayyana cewa su dai kawai suna kare kansun ne daga ’yan ta’adda.

Mai magana da yawun Rundunar Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, bai amsa tambayar da wakilinmu ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Tun da farko, Aminiya ta ruwaito cewa an kai hare-hare da dama ƙauyukan Bokkos tsakanin watan Maris da Afrilu, inda mutane da dama suka mutu.

Hukumomin tsaro sun tura jami’ansu domin wanzar da da zaman lafiya a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare Makiyaya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mutum 3, sun sace 26 a ƙauyukan Zamfara

Aƙalla mutum uku aka kashe, yayin da aka sace 26 a wani sabon harin da ’yan bindiga suka kai yankin Ƙaramar Hukumar Kaura Namoda, a Jihar Zamfara.

Harin ya faru ne daga ranar Alhamis zuwa Asabar a ƙauyukan da suka haɗa da Sabon Gari da Kungurki.

Mataimakiyar shugaban majalisar dokokin Edo ta yi murabus Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200

Wani mazaunin yankin ya ce: “Mutane sun fara barin gidajensu da daddare, suna dawowa ne da safe. Hare-haren da ake kai wa Sabon Gari da maƙwabtan ƙauyuka na ƙara tsananta.”

Ana zargin yaran wani ƙasurgumin ɗan bindiga mai suna Bello Kaura wanda aka fi sani da Dan Sade ne da kai wannan harin.

Wata majiya ta ce yana da sansani kusa da Sabon Gari.

Wani mazaunin ya ƙara da cewa: “Muna roƙon gwamnati ta kafa sansanin soja a Kungurki.

“Waɗannan ’yan bindiga na kai mana hari duk lokacin da suka ga dama, rayuwarmu tana cikin firgici.”

A wani harin da suka kai, mutum huɗu suka kashe, tare da sace wani mutum ɗaya.

Daga baya, ’yan bindigar sun nemi a biya su Naira miliyan uku a matsayin kuɗin fansa amma suka ƙi barin kowa ya ji muryar wanda suka sace.

Gwamna Dauda Lawal ya tabbatar da ƙarin goyon bayansa ga hukumomin tsaro tare da ƙaddamar da dakarun sa-kai na Community Protection Guard domin taimakawa wajen kare al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda aka kashe dan fashi aka kama wasu 7 a Abuja
  • Hare-Haren Isra’ila Ya Hallaka Aƙalla Mutum 38 A Gaza Cikin Rabin Sa’a
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3, sun sace 26 a ƙauyukan Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara
  • An kashe ’yan kasuwa 15 a wani sabon hari a Binuwai
  • Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato
  • Kotu A Iran Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan ‘Yan Ta’adda Da Suka Kai Hari Kan Hubbaren Shah Cheragh