Aminiya:
2025-09-17@22:08:06 GMT

An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato

Published: 20th, May 2025 GMT

Wasu makiyaya biyu sun rasu bayan da wasu da ba a san ko su wane ne ba suka buɗe musu wuta a kusa da ƙauyen Tahore, da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos, a Jihar Filato.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da mamatan ke dawowa daga kasuwar Maikatako a kan babur.

Yadda ’yan sanda suka kashe dan fashi suka kwato bindigogi 7 a Abuja Harin ’yan bindiga ya sa Zamfarawa sun koma kwana a jeji

Shugaban Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah a Jihar Filato, Ibrahim Yusuf Babayo, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana sunan mamatan a matsayin Umar Sa’idu da Rashida Yakubu.

Ya ce lamarin ya faru ne da yamma, kuma ya sanar da manyan jami’an tsaro ciki har da sojoji da ’yan sanda.

Babayo ya yi Allah-wadai da kisan, ya kuma roƙi hukumomin tsaro da su ɗauki mataki don hana sake faruwar irin haka a gaba.

Ya kuma buƙaci ’yan uwansa Fulani da su kwantar da hankalinsu tare da kaucewa ɗaukar doka a hannu.

“Abin da ke faruwa da al’ummarmu yana da matuƙar tayar da hankali. Mun riga mun rasa shanu sama da ɗari tare da wasu makiyaya. Yanzu kuma an kashe mana wasu biyu,” in ji shi.

Sai dai wani jigo a ƙungiyar raya al’adu ta Bokkos (BCDC), John Apollos Maton, ya ce bai da labarin faruwar harin.

Ya kuma musanta cewa mutanensu na da hannu a lamarin, inda ya bayyana cewa su dai kawai suna kare kansun ne daga ’yan ta’adda.

Mai magana da yawun Rundunar Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, bai amsa tambayar da wakilinmu ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Tun da farko, Aminiya ta ruwaito cewa an kai hare-hare da dama ƙauyukan Bokkos tsakanin watan Maris da Afrilu, inda mutane da dama suka mutu.

Hukumomin tsaro sun tura jami’ansu domin wanzar da da zaman lafiya a yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare Makiyaya

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

Ya ce ya sayi layin wayar ne daga hannun wani Audu, ɗan kungiyar Vikings wanda ya tsere yanzu.

A wani lamari kuma, ‘yansanda sun kama wasu mutum huɗu da suka shiga gonar wani mutum a Lapai Gwari, inda suka saci kifi da darajar kuɗinsu ta kai Naira 750,000.

Babban wanda ake zargi, Hussaini Garba, ya amsa laifi tare da bayyana Ahmed Yusuf, Ibrahim Musa da Abdulazeez Bawa a matsayin mutanen da suke sayen kifin idan ya sato.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000