Trump ya ce ya yi tattaunawa mai armashi da Putin
Published: 20th, May 2025 GMT
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce yayi tattaunawa ta wayar tarho mai aramashi da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin, inda suka tattauna kan batutuwa da dama ciki har da yunkurin fara tattaunawar tsagaita bude wuta nan da nan tsakanin Rasha da Ukraine.
Kamfanin dillancin labaran Rasha na RIA shi ma ya ambato, shugaban Kremlin na cewa tattaunawar ta yi amfani.
Rasha a shirye take ta yi aiki tare da Ukraine a kan wata yarjejeniya “game da samar da zaman lafiya a nan gaba.”
“Rasha da Ukraine za su fara tattaunawa nan take domin tsagaita bude wuta,” in ji Trump.
A cewar wata majiya kusa da tattaunawar da ke gudana, shugaban fadar White House ya tuntubi Volodymyr Zelensky “na ‘yan mintoci kadan” kafin kiran Putin.
“Daidaita” dangantaka, musayar fursunoni, Iran da Gabas ta Tsakiya na daga cikin batutuwan da aka tattauna.
Mr. Putin ya yaba da shawarwarin da ake yi tsakanin Washington da Tehran kan shirin nukiliyar Iran da aka faro ta hanyar shiga tsakani na Oman.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Tehran ya bukaci tattaunawa cikin gaggawa kan kalubalen yankin
Manyan jami’ai daga kasashe da dama da ke halartar taron tattaunawa na Tehran sun yi kira da a tattauna domin tunkarar manyan al’amura a yankin.
Manyan jami’ai daga kasashe 53 da suka hada da ministoci da masana da ne ke halartar taron na kwanaki biyu.
Ministan harkokin wajen Oman Badr bin Hamad Al Busaidi ya ce a halin yanzu yankin yammacin Asiya na fuskantar kalubale da dama da ke bukatar tattaunawa cikin gaggawa.
A yayin jawabin nasa, Ministan harkokin wajen Oman ya bayyana matukar damuwarsa kan tashe-tashen hankula da kisan kiyashin da al’ummar Falasdinu ke fuskanta, yana mai bayyana wannan lamari a matsayin wani abin takaici a duniya.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen kasar Tajikistan ya jaddada bukatar yin tattaunawa mai ma’ana don tinkarar manyan matsalolin da duniya ke fuskanta.
Armeniya ta bakin sakatarenta na komitin sulhu Armen Grigoryan ta tabbatar da aniyar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
Shi kuwa tsohon firaministan kasar Iraki Adel Abdul-Mahdi ya bayyana matukar damuwarsa game da matsalar jin kai da kuma ci gaba da kisan kiyashi a zirin Gaza.
Ya yi Allah wadai da gazawar kasashen Larabawa da kungiyoyin kasa da kasa, wadanda a cewarsa, sun kasa dakile irin ta’asar da Isra’ila ke yi.