Trump ya ce ya yi tattaunawa mai armashi da Putin
Published: 20th, May 2025 GMT
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce yayi tattaunawa ta wayar tarho mai aramashi da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin, inda suka tattauna kan batutuwa da dama ciki har da yunkurin fara tattaunawar tsagaita bude wuta nan da nan tsakanin Rasha da Ukraine.
Kamfanin dillancin labaran Rasha na RIA shi ma ya ambato, shugaban Kremlin na cewa tattaunawar ta yi amfani.
Rasha a shirye take ta yi aiki tare da Ukraine a kan wata yarjejeniya “game da samar da zaman lafiya a nan gaba.”
“Rasha da Ukraine za su fara tattaunawa nan take domin tsagaita bude wuta,” in ji Trump.
A cewar wata majiya kusa da tattaunawar da ke gudana, shugaban fadar White House ya tuntubi Volodymyr Zelensky “na ‘yan mintoci kadan” kafin kiran Putin.
“Daidaita” dangantaka, musayar fursunoni, Iran da Gabas ta Tsakiya na daga cikin batutuwan da aka tattauna.
Mr. Putin ya yaba da shawarwarin da ake yi tsakanin Washington da Tehran kan shirin nukiliyar Iran da aka faro ta hanyar shiga tsakani na Oman.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bude kofofin wuta a kan haramtacciyar kasar Isra’ila ta hanyar mayar da martani kan harin da yahudawan sahayoniyya suka kai kan kasarta
Iran ta bude kofofin jahannama kan ‘yan sahayoniyya a matsayin mayar da martani ga mummunan zaluncin da suka kaddamar kan lardunan Iran da dama, wanda ya yi sanadiyyar shahadan mutane da dama da jikkata.
Bayan da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Wajibi ne gwamnatin mamayar Isra’ila ta jira mummunan hukunci mai tsanani da kuma makoma mai daci kan abin da aikata, kuma bayan da sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci Manjo Janar Muhammad Pakpour ya bayyana cewa: Sojojin kasar Iran za su bude kofofin jahannama kan kisan yara kanana, Iran ta fara kaddamar da hare-haren daukan fansa mai suna “Alkawarin Gaskiya na 3”, inda ta harba makamai masu linzami na ballistic da hypersonic kan yankuna daban daban na haramtacciyar kasar Isra’ila.
A cewar faifan bidiyo da aka wallafa, hakika Iran ta kai hare-hare da makamai masu linzami kan tsakiyar birnin Tel Aviv da kuma cibiyoyi da dama na soji da sansanonin sojin saman haramtacciyar kasar Isra’ila.