Aminiya:
2025-11-02@21:13:28 GMT

Malamai sun gindaya sharaɗi kafin janye yajin aiki a Abuja 

Published: 20th, May 2025 GMT

Malaman makarantu da ma’aikatan ƙananan hukumomi a Babban Birnin Tarayya, Abuja, sun bayyana cewa ba za su janye yajin aikin da suka shiga ba, har sai an biya malaman firamare bashin albashin da suke bi.

Yajin aikin ƙarƙashin jagorancin rassan ƙungiyar malamai ta ƙasa (NUT) da ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta ƙasa (NULGE), da na Abuja.

Zulum zai saya wa sojoji da ’yan sa-kai ƙarin motoci don yaƙar Boko Haram An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya

Wani mamba a ƙungiyar, wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu ta wayar tarho cewa shugabannin ƙungiyoyin sun bayyana wannan matsaya ne a yayin wasu taruka guda biyu da suka gudanar a ranar Alhamis da kuma Juma’ar da ta gabata.

A cewarsa, shugabannin ƙananan hukumomi guda shida a Abuja, sun roƙi shugabannin ƙungiyoyin da su dakatar da yajin aikin domin ci gaba da tattaunawa, amma taron ya kare ba tare da an cimma matsaya ba.

Ƙungiyoyin sun nuna ɓacin ransu kan yadda shugabannin ƙananan hukumomi ke karya yarjejeniyar da aka cimma a baya-bayan nan, tare da rashin damuwa da walwalar malamai da sauran ma’aikatan ƙananan hukumomi.

Ko da yake ƙungiyoyin sun yaba da matakin shugabannin wajen aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi, sun ce har yanzu akwai sauran buƙatu da ba a biya ba.

Ƙungiyoyin sun kuma amince da shawarar Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, na amfani da kashi 10 na kuɗaɗen harajin da Abuja ke tattarawa daga ƙananan hukumomi domin biyan hakkokin ma’aikatan.

Sun buƙaci a fara biyan bashin watanni takwas na sabon mafi ƙarancin albashi da malamai da ma’aikatan ƙananan hukumomi ke bi, wanda adadinsa ya kai sama da Naira biliyan 16.

Sun jadadda cewar har sai an cika waɗannan sharuɗa, sannan za su janye yajin aikin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ma aikatan Ƙananan Hukumomi makarantu Sharadi Yajin aiki yajin aikin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari