Malamai sun gindaya sharaɗi kafin janye yajin aiki a Abuja
Published: 20th, May 2025 GMT
Malaman makarantu da ma’aikatan ƙananan hukumomi a Babban Birnin Tarayya, Abuja, sun bayyana cewa ba za su janye yajin aikin da suka shiga ba, har sai an biya malaman firamare bashin albashin da suke bi.
Yajin aikin ƙarƙashin jagorancin rassan ƙungiyar malamai ta ƙasa (NUT) da ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta ƙasa (NULGE), da na Abuja.
Wani mamba a ƙungiyar, wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu ta wayar tarho cewa shugabannin ƙungiyoyin sun bayyana wannan matsaya ne a yayin wasu taruka guda biyu da suka gudanar a ranar Alhamis da kuma Juma’ar da ta gabata.
A cewarsa, shugabannin ƙananan hukumomi guda shida a Abuja, sun roƙi shugabannin ƙungiyoyin da su dakatar da yajin aikin domin ci gaba da tattaunawa, amma taron ya kare ba tare da an cimma matsaya ba.
Ƙungiyoyin sun nuna ɓacin ransu kan yadda shugabannin ƙananan hukumomi ke karya yarjejeniyar da aka cimma a baya-bayan nan, tare da rashin damuwa da walwalar malamai da sauran ma’aikatan ƙananan hukumomi.
Ko da yake ƙungiyoyin sun yaba da matakin shugabannin wajen aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi, sun ce har yanzu akwai sauran buƙatu da ba a biya ba.
Ƙungiyoyin sun kuma amince da shawarar Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, na amfani da kashi 10 na kuɗaɗen harajin da Abuja ke tattarawa daga ƙananan hukumomi domin biyan hakkokin ma’aikatan.
Sun buƙaci a fara biyan bashin watanni takwas na sabon mafi ƙarancin albashi da malamai da ma’aikatan ƙananan hukumomi ke bi, wanda adadinsa ya kai sama da Naira biliyan 16.
Sun jadadda cewar har sai an cika waɗannan sharuɗa, sannan za su janye yajin aikin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ma aikatan Ƙananan Hukumomi makarantu Sharadi Yajin aiki yajin aikin
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta sanar da kammala dawo da dukkan alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana gida Najeriya daga kasar Saudiyya.
A cikin wata sanarwar da Daraktar Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta fitar ranar Laraba, ta ce jirgin karshe dauke da alhazai 88 ya bar birnin Jiddah da misalin karfe 10:30 na safe dauke da alhazan jihar Kaduna da Katsina.
Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a DeltaA cewar hukumar, hakan ya kawo karshen jigilar da aka shafe kwana 20 ana yi tun ranar 13 ga watan Yuni.
A sakonsa na bankwana ga alhazan, shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bayyana godiyarsa ga Allah kan kammala aikin cikin nasara.
Ya kuma bukaci alhazan da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’ar Allah ya kawo mata karshen tarin matsalolin da suke addabar ta.
Farfesa Abdullahi ya kuma tunatar da su cewa Aikin Hajji ibada ce da take nuna zaman lafiya da kwanciyar hankali, sannan ya buƙace su da su ci gaba da zumuncin da suka ƙulla a tsakaninsu lokacin ibadar.