HausaTv:
2025-12-10@14:45:54 GMT

Salami: Makiyan Iran Ba Su San Wani Abu Ba Sai Karfi

Published: 16th, March 2025 GMT

Kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran manjo  janar Salami wanda ya gabatar da jawabi a wurin tunawa da shahid Mahadi Bakiri a garin Tabriz ya bayyana cewa;; Babu yadda za ayi jamhuriyar musulunci ta Iran ta bude tattaunawa da Amurka a karkashin barazana, yana mai kara da cewa; yin gwawarmaya da jajurcewa a gaban masu girman kai da daga hanci, yana daga cikin muhimman koyarwar alkur’ani mai girma da kuma tsarin musulunci.

Manjo janar Salami ya kara da cewa; ta hanyar tsayin daka da dunkulewar al’umma wuri daya, za a kai ga samun nasara.

Haka nan ya kara da cewa; A tsawon shekaru 46 da su ka gabata, al’ummar Iran ta kasance a cikin fadaka wajen fuskantar duk wata barazana.

Bugu da kari kwamandan dakarun kare juyin juya halin musuluncin na Iran ya kuma ce; Makiyan jamhuriyar musulunci ta Iran masu kekashewar zukata ne, ba su aiki da mandiki, kuma ba su aiki da duk wata halayya ta ‘yan ta ‘yan adamtaka,abu daya tilo da su ka yi imani da shi, shi ne amfani da karfi.

Har ila yau, kwamandan dakarun kare juyin musuluncin na Iran ya yi ishara da halayyar HKI da Amurka a yakin Gaza, Lebanon, Syria, Yemen, Iraki da Afghanistan; yana mai kara da cewa; sun tabbatar da cewa, su masu karya alkawali ne, don haka batun tattaunawa da  wadannan makiyan  kuskure ne

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kara da cewa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga 18 Sun Muta a Wata Arangama da Rundunar Operation Fansan Yamma

Daga Nasir Malali

An kashe ’yan bindiga guda goma sha takwas a wani samame da Rundunar Hadin Gwiwa ta Operation Fansan Yamma ta kai a kauyen Kurawa da ke Karamar Hukumar Sabon Birni ta Jihar Sokoto.

A wata hira ta wayar tarho, wani shaida daga yankin, Malam Aminu Muhammad, ya shaida wa Rediyon Najeriya a Sokoto cewa, nasarar samamen ta fara ne bayan rundunar ta samu bayanin cewa wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da mazauna yankin da ke kan hanyarsu ta zuwa kasuwar mako-mako a kan hanyar Tarah zuwa Karawa a Sabon Birni.

Sojojin sun garzaya cikin gaggawa bayan jin harbe-harbe, inda suka kusan awa guda suna musayar wuta da maharan.

Shaidan gani da idon ya ce sojojin sun  kwato bindigogi da babura takwas, tare da tabbatar da cewa babu jami’in tsaro ko farar hula da ya rasa ransa ko ya ji rauni a samamen.

Da aka tuntube shi ta waya, dan majalisar dokoki mai wakiltar Sabon Birni a Majalisar Dokokin Jihar Sokoto, Honarabul Aminu Boza, ya tabbatar da lamarin, yana mai cewa rundunar hadin gwiwar na ci gaba da gudanar da aikin bincike a maboyar ’yan bindigar tare da taimakon wani dan bindiga da aka kama wanda ke nuna wa sojojin hanya a yayin binciken.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • ‘Yan Bindiga 18 Sun Muta a Wata Arangama da Rundunar Operation Fansan Yamma
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici
  • Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya
  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja