Sakamakon Neman ’Yancin Taiwan Zai Kai Yankin Ga Halaka
Published: 15th, March 2025 GMT
A baya-bayan nan, jagoran ‘yan awaren Taiwan Lai Ching-te, wanda ya kira kansa da “mai rajin neman ‘yancin kan Taiwan”, ya kara ikirarin cewa bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan ba sa karkashin ikon juna, har ma ya ce wai Taiwan wata kasar demokradiyya ce mai mulkin kanta. Amma duk yunkurin Lai Ching-te ba zai iya canza gaskiyar da duniya ta amince da ita ba, wato Taiwan ba ta taba zama kasa ba, kuma ba za ta taba zama ba a nan gaba.
Ta yaya za a warware batun Taiwan? Tuni dai babban yankin kasar Sin ya tabbatar da cewa, a shirye yake ya yi iyakacin kokari da sahihiyar zuciya domin neman kyakkyawar makomar dinkewar kasar Sin cikin lumana. Amma idan ‘yan aware masu neman “’yancin Taiwan” suka yi tsokana ko tilasta neman ballewa ko ma tabo batu mai tada kura, dole ne zai dauki matakai masu tsauri. Lai Ching-de da mabiyansa da ke wasa da wuta a mashigin tekun Taiwan, za su kone kansu. Sin za ta hada yankunanta, kuma tabbas za su dunkule. Wannan shi ne yanayin tarihi da ba za a iya juyawa ba. (Mai fassara: Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
Gwamnatin kasar Saudiya ta yi allawadai da HKI a kissan da take wa falasdinawa a Gaza, a jiya talata a gaban kutun ICJ. Saudiya ta bayyana cewa gwamnatin HKI ta sabawa dokokin kasa da kasa da dama a kissan kiyashin da take yi a Gaza.
Wakilin kasar a gaban kotun Muhammad Saud Al-Nasser, ya kara da cewa, HKI ta ci gaba ta sabawa wadannan dokoki, amma kuma bata da dalilan saba masu.
Banda kissan kiyashin da take yi a Gaza, Al-Nasser ya ce HKI ta maida Gaza kofai, ta rusa mafi yawan gine-ginen yankin, sannan ta hana shigowar abinci da ruwa da magunguna zuwa yankin, wadanda ko wane daya daga cikinsu take hakkin bil’adama ne wanda yake kaiwa ga laifin yaki.
Gwamnatin Saudiya ta gabatar da wannan jawabin ne a rana ta biyu da bude zaman da kotun ta ICJ tayi don tattaunwa da kuma jin ra’ayin kasashe dangane da take hakkin bi’adaman da HKI take yi a Gaza. A halin yanzu fiye da kwamaki 50 kenan da gwamnatin HKI ta ke hana shigowar abinci da magunguna da kuma bukatun falasdinawa zuwa yankin.
Har’ila yau kotun ta girka wannan zaman ne don tattauna yadda HKI take mu’amala da umurnin ta danganda take hakkin bil’adama a Gaza.