Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-20@16:05:30 GMT

Kwara Ta Kafa Tutar Hadin Kai Mai Mita 70 A Ilorin

Published: 20th, May 2025 GMT

Kwara Ta Kafa Tutar Hadin Kai Mai Mita 70 A Ilorin

Gwamnatin jihar Kwara ta kafa tutar hadin kai mai tsayin mita 70 a hukumance, wanda ke zama alamar “hadin kan kasa, tafiya tare da buri a matsayin al’umma”.

 

Da yake jawabi a wani takaitaccen biki a Ilorin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya ce jihar ba ta daga tuta kawai ba, a’a tana nuna kwarin guiwar wata alama ce ta hadin kai, alfahari, da kuma kishin kasa.

 

Gwamnan ya samu wakilcin kwamishinan sadarwa na jihar Bola Olukoju, wanda wasu kwamishinoni uku suka taimaka masa: Aliyu Kora Sabi (sufuri); Nafisat Buge (Muhalli); da Nnafatima Imam (ci gaban al’umma) da sauran manyan baki.

 

A cewarsa, sandar tuta na kara karfafa martabar jihar a matsayin cibiyar kirkire-kirkire, al’adu, da jagoranci mai ma’ana.

 

Gwamna Abdulrazaq ya yi bayanin cewa, alamar za ta zama babban abin jan hankali, jawo masu ziyara, da samar da damammaki, da kuma baje kolin dabarun saka hannun jari na jihar kan ababen more rayuwa da ba wai kawai a yi amfani da su ba har ma da karfafa gwiwa.

 

Ya ce gwamnatinsa ta gina tituna, asibitoci na zamani, da karfafa samar da ruwan sha tare da bayar da tallafi ga manoma, ‘yan kasuwa, da kuma bangarori daban-daban na al’umma.

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su

Gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq ya aika ta’aziyya ga iyalan mutane 37 da hatsarin kwale-kwalen Gbajibo ya rutsa da su daga jihar Neja a karshen mako.

 

A cikin sanarwar gwamna AbdulRazaq ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Neja kan wannan lamari mai ban tausayi.

 

Gwamnan ya bukaci ma’aikatan jirgin da fasinjoji da su bi ka’idojin tsaro domin amfanin kowa.

 

Ya bayyana a matsayin al’ada mai raɗaɗi kuma ba za a yarda da ita ta rashin amfani da na’urorin kariya da gwamnati ta bayar akai-akai.

 

Yana rokon Allah ya jikan wadanda aka kashe.

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo
  • Hadin Gwiwa Bisa Daidaito Da Girmama Juna Tsakanin Sin Da Amurka Zai Samar Da Moriyar Juna
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Kan Tsibiran Kasarta
  • Kano Za Ta Yaki Cutar Hawan Jini Tare Da Hadin Gwiwar Kungiyar Global Effort
  • Ciwon Mara Lokacin Al’ada
  • Hajji: Gwamnatin Katsina ta biya wa maniyyata 2000 kuɗin hadaya
  • Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
  • Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa