Hare-Haren Isra’ila Ya Hallaka Aƙalla Mutum 38 A Gaza Cikin Rabin Sa’a
Published: 20th, May 2025 GMT
Akalla Falasdinawa 38 ne suka rasa rayukansu a wani jerin hare-haren jiragen yaƙin Isra’ila da aka kai a sassa daban-daban na Gaza cikin rabin sa’a da dare, in ji likitocin Falasɗinawa.
Rahotanni daga hukumar agajin gaggawa da ke ƙarkashin Hamas sun ce jiragen yaƙin Isra’ila sun kai hari a wurare da dama, ciki har da wata makaranta a gabashin birnin Gaza, da kuma wani tsohon gidan mai a sansanin ’yan gudun hijira na Nuseirat da ke tsakiyar Gaza, inda iyalai da dama ke neman mafaka.
Hukumar ta ƙara da cewa tawagar ceto na fuskantar matsaloli wajen kai ɗauki ga waɗanda suka jikkata saboda ƙarancin kayan aiki da kuma tsananin harin.
Wannan hari ya biyo bayan umarnin kwashe jama’a gaba ɗaya da Isra’ila ta bayar a wani shiri na kai “mummunan hari da ba a taɓa gani ba,” a cewarta.
A cewar wasu masu rajin kare haƙƙin dan Adam a birnin Gaza, mutum 10 ne suka mutu a lokacin da wani hari da jirgi a makarantar Musa bin Nusayr inda ɗaruruwan ’yan gudun hijira ke fakewa.
A tsakiyar Gaza, rahotanni sun ce mutum 15 sun mutu a wani hari da aka kai kan tantuna a wani tsohon gidan mai da ke sansanin Nuseirat.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
Rahotanni sun bayyana cewa gwamnatin isra’ila na fuskantar suka game da matakin da ta dauka na kai hari kan kungiyar unicef ta majalisar dinkin duniya a gaza, matakin da falasdinawa da masu sa ido ke gani a matsayin wata dabara ta murukushe kungiyoyin agaji da kuma fitar da kungiyoyin majalisar dinkin duniya daga yankin gaza
Rahoton da wani jami’in majalisar dinkin duniya ya fitar a jiya jumaa ya nuna cewa sojojin isra’ila sun kama wani ma’aikacin UNICEF mai suna Raed Afif mai shekaru 45 da haihuwa a kerem shalom alokacin da yake gudanar da ayyukansa.
Yazu wa yanzu isra’ila bata bayyana dalilan da suka sanya ta kama shi ba kuma take ci gaba da tsare shi.
Kwana daya kafin tayi kamun isra’ila ta bukaci kungiyar ta Unicef da ta kwashe dukkan kayayyakin agajinta daga yankin , kawai sai ta rufe dukkan kofofin shiga da magunguna zuwa asibitocin dake arewacin yankin Gaza. Kungiyoyin bada agaji na duniya sun yi gargadin cewa wannan matakin an dauke shi ne domin yanke duk wasu ayyukan jinkai da ake yi da kuma korar dukkan kungiyoyin agaji da hakan zai kara sanyawa yanayi ya kara tazzar a yankin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci