Mai dakin Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta sake jaddada kudurin gwamnatin jihar na ganin an kawar da tu’ammali da miyagun kwayoyi a fadin jihar.

Ta bayyana hakan ne a lokacin da ta karɓi shugabannin Hukumar Yaki da Shan Miyagun Kwayoyi da Hana Safarar Mutane ta Jihar Zamfara, waɗanda suka kai mata ziyarar ban girma a fadar gwamnati da ke Gusau.

Hajiya Huriyya ta bayyana shirinta na yin aiki kafada da kafada da hukumar, domin gano ingantattun hanyoyin da za su taimaka wajen yaki da shan miyagun kwayoyi a fadin jihar.

“Muna shirin zama tare domin duba hanyoyin da za mu bi wajen magance matsalolin da kuke fuskanta, domin muna da aniyar ganin Zamfara ta nisanta daga illar tu’ammali da miyagun kwayoyi In Shaa Allah.”

Uwargidar Gwamnan ta yaba da jajircewar shugabancin hukumar, tare da tabbatar da cewa ofishinta a bude yake don hadin gwiwa a kokarin inganta rayuwar al’ummar jihar.

Ta kuma taya hukumar murna bisa nasarorin da ta samu a yayin gudanar da aikinta.

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Yaki da Shan Miyagun Kwayoyi da Hana Safarar Mutane ta Jihar Zamfara, Malam Ibrahim Ishaq Anka, ya bayyana cewa manufar ziyarar ita ce domin bayyana ci gaban da hukumar ta samu da kuma kalubalen da take fuskanta wajen aiwatar da aikinta.

“A ranar 1 ga watan Maris na wannan shekarar, mun karɓi jimillar mutane 52 da aka kama ana kokarin safararsu. Sojojin Najeriya ne suka cafke su a tsakanin Abuja da Jihar Kogi,” inji shi.

Malam Anka ya bayyana cewa hukumar ta gudanar da gangamin wayar da kai sosai kan illolin amfani da miyagun kwayoyi.

“Mun kuma shirya zaman wayar da kai da manyan limamai a fadin kananan hukumomi bakwai kan illolin amfani da kwayoyi, amfani da su ba bisa ka’ida ba, da kuma barazanar safarar mutane.”

Malam Anka ya bayyana wasu muhimman bukatun hukumar da suka hada da cibiyar gyaran hali, motocin aiki, gidajen kwanan jami’anta, da wasu muhimman kayayyakin aiki.

 

Daga Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: da miyagun kwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Jihar Jigawa Ce Ta Fara Biyan Kudaden Kujerun Aikin Hajjin 2026- NAHCON
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29