Mai dakin Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta sake jaddada kudurin gwamnatin jihar na ganin an kawar da tu’ammali da miyagun kwayoyi a fadin jihar.

Ta bayyana hakan ne a lokacin da ta karɓi shugabannin Hukumar Yaki da Shan Miyagun Kwayoyi da Hana Safarar Mutane ta Jihar Zamfara, waɗanda suka kai mata ziyarar ban girma a fadar gwamnati da ke Gusau.

Hajiya Huriyya ta bayyana shirinta na yin aiki kafada da kafada da hukumar, domin gano ingantattun hanyoyin da za su taimaka wajen yaki da shan miyagun kwayoyi a fadin jihar.

“Muna shirin zama tare domin duba hanyoyin da za mu bi wajen magance matsalolin da kuke fuskanta, domin muna da aniyar ganin Zamfara ta nisanta daga illar tu’ammali da miyagun kwayoyi In Shaa Allah.”

Uwargidar Gwamnan ta yaba da jajircewar shugabancin hukumar, tare da tabbatar da cewa ofishinta a bude yake don hadin gwiwa a kokarin inganta rayuwar al’ummar jihar.

Ta kuma taya hukumar murna bisa nasarorin da ta samu a yayin gudanar da aikinta.

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Yaki da Shan Miyagun Kwayoyi da Hana Safarar Mutane ta Jihar Zamfara, Malam Ibrahim Ishaq Anka, ya bayyana cewa manufar ziyarar ita ce domin bayyana ci gaban da hukumar ta samu da kuma kalubalen da take fuskanta wajen aiwatar da aikinta.

“A ranar 1 ga watan Maris na wannan shekarar, mun karɓi jimillar mutane 52 da aka kama ana kokarin safararsu. Sojojin Najeriya ne suka cafke su a tsakanin Abuja da Jihar Kogi,” inji shi.

Malam Anka ya bayyana cewa hukumar ta gudanar da gangamin wayar da kai sosai kan illolin amfani da miyagun kwayoyi.

“Mun kuma shirya zaman wayar da kai da manyan limamai a fadin kananan hukumomi bakwai kan illolin amfani da kwayoyi, amfani da su ba bisa ka’ida ba, da kuma barazanar safarar mutane.”

Malam Anka ya bayyana wasu muhimman bukatun hukumar da suka hada da cibiyar gyaran hali, motocin aiki, gidajen kwanan jami’anta, da wasu muhimman kayayyakin aiki.

 

Daga Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: da miyagun kwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Jaddada Kawo Karshen Bakar Siyasar gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Kan Al’ummar Falasdinu

Iran ta yi kira da a kawo karshen neman shafe wata al’umma daga kan doron kasa tare da kawo karshen rashin hukunta shugabannin ‘yan sahayoniyya

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan hare-hare da laifukan da gwamnatin ‘yan sahayoniyya take ci gaba da yi a cikin ‘yan kwanakin nan a zirin Gaza, yana mai kira da a kawo karshen kisan kiyashi da rashin hukunta shugabannin gwamnatin ‘yan shayoniyya da kuma gurfanar da su a gaban kuliya don hukunta su.

Baqa’i ya yi ishara da laifuffukan da ba a taba ganin irinsa ba da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta yi kan al’ummar Falastinu da ba su da kariya a Gaza da Yammacin Gabar Kogin Jordan, ya kuma yi kakkausar suka kan munanan hare-haren da aka kai kan matsugunan ‘yan gudun hijira na wucin gadi da cibiyoyin kiwon lafiya a Gaza, wanda ya yi sanadin shahada da jikkata daruruwan mutane a cikin ‘yan kwanakin da suka gabata. Ya yi nuni da alhakin kai tsaye da ke wuyan masu kare gwamnatin ‘yan mamaya da magoya musu baya a fagen soja da na siyasa, musamman Amurka da Birtaniya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya ce: “A halin da ake ciki, bayan gaza cimma matsaya a yunkurin masu shiga tsakani na cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta, ‘yan mamaya sun kara zafafa kai hare-haren ta’addanci da nufin gabatar da wasu bukatu da ba su dace ba, da kuma raba mazauna yankin Zirin Gaza da muhallinsu, wanda tabbas hakan zai fuskanci turjiya daga al’ummar Falasdinu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Tsaro
  • Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200
  • Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya ba su kyautar Riyal 200
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su
  • APC Ta Zargi Gwamnan Zamfara Da Shirga Karya Tare Da Kiran Ya Nemi Afuwar Zamfarawa
  • Gwamnatin Kano ta dakatar da haska shirin Labarina da Dadin Kowa da wasu 20
  • Hajji: Gwamnatin Katsina ta biya wa maniyyata 2000 kuɗin hadaya
  • Iran Ta Jaddada Kawo Karshen Bakar Siyasar gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Kan Al’ummar Falasdinu
  • Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa