Mai dakin Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta sake jaddada kudurin gwamnatin jihar na ganin an kawar da tu’ammali da miyagun kwayoyi a fadin jihar.

Ta bayyana hakan ne a lokacin da ta karɓi shugabannin Hukumar Yaki da Shan Miyagun Kwayoyi da Hana Safarar Mutane ta Jihar Zamfara, waɗanda suka kai mata ziyarar ban girma a fadar gwamnati da ke Gusau.

Hajiya Huriyya ta bayyana shirinta na yin aiki kafada da kafada da hukumar, domin gano ingantattun hanyoyin da za su taimaka wajen yaki da shan miyagun kwayoyi a fadin jihar.

“Muna shirin zama tare domin duba hanyoyin da za mu bi wajen magance matsalolin da kuke fuskanta, domin muna da aniyar ganin Zamfara ta nisanta daga illar tu’ammali da miyagun kwayoyi In Shaa Allah.”

Uwargidar Gwamnan ta yaba da jajircewar shugabancin hukumar, tare da tabbatar da cewa ofishinta a bude yake don hadin gwiwa a kokarin inganta rayuwar al’ummar jihar.

Ta kuma taya hukumar murna bisa nasarorin da ta samu a yayin gudanar da aikinta.

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Yaki da Shan Miyagun Kwayoyi da Hana Safarar Mutane ta Jihar Zamfara, Malam Ibrahim Ishaq Anka, ya bayyana cewa manufar ziyarar ita ce domin bayyana ci gaban da hukumar ta samu da kuma kalubalen da take fuskanta wajen aiwatar da aikinta.

“A ranar 1 ga watan Maris na wannan shekarar, mun karɓi jimillar mutane 52 da aka kama ana kokarin safararsu. Sojojin Najeriya ne suka cafke su a tsakanin Abuja da Jihar Kogi,” inji shi.

Malam Anka ya bayyana cewa hukumar ta gudanar da gangamin wayar da kai sosai kan illolin amfani da miyagun kwayoyi.

“Mun kuma shirya zaman wayar da kai da manyan limamai a fadin kananan hukumomi bakwai kan illolin amfani da kwayoyi, amfani da su ba bisa ka’ida ba, da kuma barazanar safarar mutane.”

Malam Anka ya bayyana wasu muhimman bukatun hukumar da suka hada da cibiyar gyaran hali, motocin aiki, gidajen kwanan jami’anta, da wasu muhimman kayayyakin aiki.

 

Daga Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: da miyagun kwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Jigawa Ta Isa Roni A Ci Gaba Da Rangadin Kananan Hukumomi

Kwamatin Harkokin Kananan Hukumomi na Majalisar Dokokin jihar Jigawa ya fara rangadin kwanaki biyu a karamar hukumar Roni a ci gaba da rangadin kananan hukumomin jihar 27 da kwamatin ya kaddamar.

A jawabin sa a sakatariyar karamar hukumar Roni, Shugaban kwamatin Alhaji Aminu Zakari, ya ce tsarin mulkin kasa ya bai wa majalisa ikon dubawa da kuma tantance yadda bangaren zartaswa ke aiwatar da manufofi da shirye shiryen gwamnati.

Ya ce ziyarar za ta mayar da hankali ga dubawa da kuma tantance kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin kudi da suka hada da kundin kasafin kudi na shekarar 2024 zuwa 2025 da Asusun kula da matsalolin muhalli da kundin bayanan kwamitocin karamar hukumar da takardun biyan kudade wato Voucher domin tabbatar da bin tanade tanaden kashe kudaden gwamnati kamar yadda ya kamata.

Alhaji Aminu Zakari ya kara da cewar a rana ta biyu kwamatin zai duba ayyukan raya kasa da karamar hukumar Roni ta gudanar daga watan Oktobar 2024 kawo yanzu sannan a karbi rahoton Yan kwamatin wadda hakan zai bada cikakkiyar fahimta game da halin da karamar hukumar ta ke ciki.

Kazalika, yace ziyarar za ta bada damar ganawa tsakanin ‘yan kwamatin da bangaren zartaswa da na kansiloli da ma’aikata domin karfafa wanzuwar dabi’ar aiki tare da kuma kyakkyawar alaka a tsakanin bangarorin karamar hukumar.

A jawabin sa na maraba, shugaban karamar hukumar Roni Dr. Abba Ya’u, ya bayyana amannar cewar ziyarar kwamatin za ta kawo gyara wajen gudanar da mulkin kananan hukumomi.

Dr. Abba ya kuma bayyana kudurin sa na aiki da shawarwarin kwamatin domin kawo cigaban karamar hukumar.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Jigawa Ta Isa Roni A Ci Gaba Da Rangadin Kananan Hukumomi
  • Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro
  • An Hori Ma’aikatan Lafiya Su Kara Kokari Wajen Rike Aikin su
  • Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Iran Ta Bayyana Lokacin Ci Gaba Da Ayyukan Cibiyoyinta Ta Nukiliya
  • Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar
  • Karamar Hukumar Maru Ta Bukaci A Dauki Matakan Kariya Kan Cutar Kwalaraci
  • Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta
  • An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
  • Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
  • Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma