An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya
Published: 20th, May 2025 GMT
Jami’an tsaron ƙasar Saudiyya sun kama wasu mata biyu da ake zargin cewa mata da kuma mahaifiyar jagoran ’yan bindiga da gwamnatin Najeriya ke nema ruwa a jallo, Ado Aliero, bayan sun je aikin Hajji.
An kama matar Aliero da mahaifiyar tasa ne a birnin Madina bayan sun je yin ziyara gabanin fara aikin Hajji.
Ado Aliero shugaban ’yan bindiga ne da ya yi ƙaurin da yin garkuwa da mutane masu yawa a lokaci guda, musamman a Jihar Zamfara da maƙwabtanta.
Kafar yada labarai ta ABN News ta bayyana cewa matan biyu sun canza sunayensu domin kada a gane su.
An cimma matsaya kan dakatar da haska fina-finai 22 a Kano Yadda Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5Kamen nasu ya zama wani sabon a yadda gwamnatin Najeriya ke aiki tare da ƙasashen duniya wajen magance matsalar ta’addanci.
An bayyana cewa Gwamnatin Najeriya tana aiki tare da Saudiyya a yayin da ake zurfafa bincike kan matan da ake zargi.
Ba a bayyana sunayen matan a hukumance ba, amma majiyoyin tsaro sun bayyana cewa akwai yiwuwar a tatsi muhimman bayanai daga gare su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
Danja ya ce, sojojin a yayin da suke aiki da sahihan bayanan sirri dangane da shirin kai hari kan al’ummar Chanchangi da kungiyar ta’adda ta Bojo ke shirin yi a ranar 15 ga Satumba, 2025, sun yi artabu da ‘yan ta’addan a kan hanyar Demeva zuwa Chanchangi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp