An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya
Published: 20th, May 2025 GMT
Jami’an tsaron ƙasar Saudiyya sun kama wasu mata biyu da ake zargin cewa mata da kuma mahaifiyar jagoran ’yan bindiga da gwamnatin Najeriya ke nema ruwa a jallo, Ado Aliero, bayan sun je aikin Hajji.
An kama matar Aliero da mahaifiyar tasa ne a birnin Madina bayan sun je yin ziyara gabanin fara aikin Hajji.
Ado Aliero shugaban ’yan bindiga ne da ya yi ƙaurin da yin garkuwa da mutane masu yawa a lokaci guda, musamman a Jihar Zamfara da maƙwabtanta.
Kafar yada labarai ta ABN News ta bayyana cewa matan biyu sun canza sunayensu domin kada a gane su.
An cimma matsaya kan dakatar da haska fina-finai 22 a Kano Yadda Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5Kamen nasu ya zama wani sabon a yadda gwamnatin Najeriya ke aiki tare da ƙasashen duniya wajen magance matsalar ta’addanci.
An bayyana cewa Gwamnatin Najeriya tana aiki tare da Saudiyya a yayin da ake zurfafa bincike kan matan da ake zargi.
Ba a bayyana sunayen matan a hukumance ba, amma majiyoyin tsaro sun bayyana cewa akwai yiwuwar a tatsi muhimman bayanai daga gare su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
Dakarun sojin Nijeriya sun yi nasarar kashe wasu ’yan ta’adda yayin wani samame da suka kai garin Kunchin Kalgo a ƙaramar hukumar Tsafe da ke Jihar Zamfara.
A sanarwar da rundunar ta wallafa a shafinta na X ranar Alhamis, ta ce a ranar 10 ga watan Yuni ne rundunar FANSAN YAMMA ta kashe ƙasurguman ‘yan ta’addan da suka haɗa da Auta da Abdul Jamilu da kuma Salisu.
Leroy Sane ya koma Galatasaray Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu“Waɗannan ’yan ta’adda suna da alaƙa da ayyukan tashin hankali da ta’addanci da ake yawan samu a yankin gaba ɗaya.
“Wannan farmakin dai na nuni da wani gagarumin koma baya ga masu aikata laifuka, wanda ke dagula zaman lafiya da tsaro a yankin,” in ji sanarwar.
Bayanan sirri na farko-farko sun nuna cewa an kashe ƙarin wasu shugabannin ’yan ta’adda, ciki har da wani da aka fi sani da Babaye a lokacin harin.
Kazalika, a wani lamarin daban, rahotanni sun ce an kashe Sale Ado Madele da aka fi sani da Sarki, babban ɗan shugaban ‘yan bindiga Ado Alieru.
A wani lamarin mai kama da haka, sojojin sun kuma kashe wasu ’yan ta’adda goma da suka taru a kusa da wata tashar mai da ke garin Danjibga.
Ana kyautata zaton ‘yan ta’addan na cikin wani gungun hadin-gwiwa da Dogo Sule ya haɗa domin kai hari.
Rundunar sojojin Nijeriya ta ce tana ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da kuma maido da dauwamammen zaman lafiya a fadin Jihar Zamfara da yankin Arewa maso Yamma.
“Wannan aiki yana ƙara jaddada ƙudurinmu na wargaza hanyoyin sadarwar ‘yan ta’adda tare da gurfanar da masu aikata laifuka a gaban ƙuliya.