HausaTv:
2025-05-20@14:30:22 GMT

Yeman ta yi barazanar killace tashar jiragen ruwan Haifa ta Isra’ila

Published: 20th, May 2025 GMT

Yemen ta yi barazanar killace babbar tashar jiragen ruwan Haifa ta Isra’ila, tare da gargadin cewa jiragen ruwa da ke tafiya a can.

“Dukkan kamfanonin da jiragensu ke nan ko kuma suka nufi wannan tashar, ana sanar da su cewa, ya zuwa wannan sanarwar, an saka tashar cikin jerin wuraren da muke son kaiwa hari,” in ji kakakin kungiyar Ansarullah da aka fi sani da ta ‘yan Houthi a Yemen Yehya Saree.

Rundunar sojin Yeman ta ce kakaba takunkumi na a matsayin mayar da martani ga yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan yankin Zirin Gaza da aka yi wa kawanya.  

Sanarwar ta ce sojojin Yemen ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen daukar karin matakai na goyon bayan al’ummar Falastinu da ake zalunta da kuma tsayin daka.

Rundunar ta jaddada cewa matakan na Yemen za su zo karshe da zarar an kawo karshen hare-haren wuce gona da iri kan Gaza tare da dage shingen da aka yi Zirin.

Tun da farko dama wani babban jami’in kasar Yemen ya gargadi kamfanonin jiragen sama na kasuwanci na kasa da kasa dake zirga-zirgar zuwa filin jirgin sama na Ben Gurion da ke yankunan da Isra’ila ta mamaye a yayin da ake ci gaba da kai hare-hare na ramuwar gayya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Halaka Sojojin Sahayoniyya Tare Da Jikkata Wasu A Beit Lahiya

Wani harin kwanton bauna da rundunar sojin al-Qassam suka kai kan sojojin mamayar Isra’ila a Beit Lahiya ya yi sanadiyar halaka tare da jikkatan sojojin mamaya masu yawa

Rundunar Izzuddeen al-Qassam bangaren sojin kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas, ta sanar da cewa: Mayakanta sun kai wani kazamin harin kwantan bauna a yankin al-Atatra da ke yammacin Beit Lahiya a arewacin zirin Gaza, inda suka yi nasarar ritsawa da sojojin mamaya masu yawa da suka yi sanadaiyyar halakar wasu daga cikinsu bayan jikkata wasu da dama.

Rundunar ta Al-Qassam ta ce: Mayakanta sun kai hari kan motocin sojin mamayar Isra’ila uku da bama-baman Shawaz guda biyu da kuma makami mai linzami, sannan kuma suka yi arangama da wata rundunar mamayar Isra’ila.

Dangane da sakamakon farmakin, rundunar ta al-Qassam ta bayyana cewa: Mayakanta sun kashe tare da raunata sojojin mamayar Isra’ila tare da nuna yadda jiragen sama masu saukar ungulu suke jigilar wadanda suka halaka da jikkata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ba Ta Da Alkiblar Siyasa
  • Hare-Haren Wuce Gona Da Irin Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Halaka Sojojin Sahayoniyya Tare Da Jikkata Wasu A Beit Lahiya
  • Wasu Shugabannin Turai Sun Yi Barazanar Ladabtar Da Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Hare-Haren Isra’ila Ya Hallaka Aƙalla Mutum 38 A Gaza Cikin Rabin Sa’a
  • Isra’ila Ta Kai Hari Ga Rumbun Magungunna A Kudancin Gaza
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : Hare-haren da Isra’ila ta kai kan Yemen babban laifin yaki ne
  • Yemen ta sake harba makami mai linzami kan Isra’ila