Leadership News Hausa:
2025-05-20@00:02:48 GMT

Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA

Published: 20th, May 2025 GMT

Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, yankin Taiwan na kasar Sin ba shi dalili ko iko ko kuma hujjar halartar babban taron hukumar lafiya ta duniya (WHA), har sai sai gwamnatin tsakiya ta kasar ta amince masa.

Kakakin ma’aikatar ne ya bayyana haka yau Litinin, lokacin da yake tsokaci kan matakin da WHA ta dauka na kin sanya bukatar Taiwan ta halartar taron a matsayin ‘yar kallo, cikin ajandarta.

A cewar kakakin, an shafe wani lokaci yanzu, hukumomin jam’iyyar DPP da wasu kasashe suna kokarin mayar da hannu agogo baya, inda suke kalubalanta da kokarin hargitsa kudurin MDD mai lamba 2758, domin kalubalantar manufar Sin daya tak a duniya. Ya ce, wannan ba kalubale ne ga cikkaken ‘yancin kasar Sin da iko kan yankunanta ba, kalubale ne ga matsaya ta adalci da kasa da kasa suka cimma da kuma tsarin odar duniya, bayan yakin duniya na II. Ya ce, kasa da kasa sun amince da matakin Sin na kin amincewa Taiwan ta halarci taron na bana, lamarin da ya nuna cewa, yarda da manufar Sin daya tak a duniya, shi ne burin al’umma da ya dace da yanayin da ake ciki, kuma shi ne abu mafi dacewa. Bugu da kari, kakakin ya ce, yadda kasa da kasa suka amince da manufar kasar Sin daya tak a duniya, abu ne da ba za a iya kalubalanta ba. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kafofin Yada Labarai Na Amurka Sun Bayyana Kuzari Da Ci Gaban Da Fina-finan Kasar Sin Ke Samu A Bikin Cannes 

Kamar yadda mujallar ta bayar da rahoto a kai, rumfar fina-finai ta kasar Sin ta zama wata alama da ke nuna yadda kasar Sin ke ci gaba da kyautata cudanyar al’adu da hadin gwiwar kasa da kasa a harkar fina-finai. Kana, bisa samun karuwar jawo hankulan kasashen duniya da kuma kafa kwakkwarar turbar fasahar kirkira ta gwaninta da iya tsara labarin fim, sashen fina-finan na kasar Sin ya mike haikan wajen taka rawa sosai a duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Kan Tsibiran Kasarta
  • Kano Za Ta Yaki Cutar Hawan Jini Tare Da Hadin Gwiwar Kungiyar Global Effort
  • Fira Ministan Libiya Ya Tantance Bangarorin Da Kula Da Hakkin Tsaron Kasar Ya Rataya A Wuyarsu
  • Taron Tehran ya bukaci tattaunawa cikin gaggawa kan kalubalen yankin  
  • Kafofin Yada Labarai Na Amurka Sun Bayyana Kuzari Da Ci Gaban Da Fina-finan Kasar Sin Ke Samu A Bikin Cannes 
  • Shuwagabanin Larabawa Sun Yi Alkawalin Sake Gina Gaza, Suna Kuma Kokarin Tsagaita Wuta Da Farko
  • Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada
  • Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa