Gwamnatin kasar Masar na shirin yin arangama ta soji da haramtacciyar kasar Isra’ila

Kafofin yada labaran Isra’ila, musamman tashar talabijin ta 14, sun watsa wani rahoto cewa: Gwamnatin kasar Masar na kokarin karfafa karfinta na soji a tsibirin Sinai, tana mai gargadin abin da ta bayyana a matsayin “yiwuwar rugujewar yarjejeniyar zaman lafiya” da aka rattaba hannu tsakanin kasashen biyu a shekara ta 1979.

Tashar talabijin ta NAN ta nakalto Eliyahu Dekel, tsohon shugaban hukumar leken asirin sojin haramtacciyar kasar Isra’ila kuma masani kan al’amuran Masar na cewa: Masar na cikin gaggawar shirin tunkarar rikicin soji, yana mai cewa “yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla tsakanin kasashen biyu a shekarar 1979 ta kasance cikin yanayi na rugujewa tun lokacin da aka rattaba hannu kan yarjejeniyar, kuma babu wata magana daya da ba a karya ba,” in ji shi.

A wata hira da aka yi da shi kan shirin na Oded Menashe, Dekel ya kara da cewa, nazarin hotunan tauraron dan adam ya nuna yadda ake gina filayen tashi da saukar jiragen sama na soja guda uku a yankin Sinai, baya ga gada da mashigar ruwa kusan 60 da ke kan mashigin Suez, yana mai bayyana hakan a matsayin wani yanayi na soji mai cike da damuwa.

Ya yi nuni da cewa, tun a shekara ta 2007, Masar ta kara kaimi kan ayyukan soji a yankin, wanda ya yi la’akari da shi a matsayin “shirin da take yi na yiyuwar arangama da sojojin mamayar Isra’ila.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Fira Ministan Libiya Ya Tantance Bangarorin Da Kula Da Hakkin Tsaron Kasar Ya Rataya A Wuyarsu

Fira ministan gwamnatin rikon kwaryar Libiya ya bayyana cewa: Babu wata cibiyar tsaro a Libya sai dai cibiyoyi na yau da kullum da suka hada da sojoji da ‘yan sanda

Abdul Hamid Dbeibah, shugaban gwamnatin rikon kwaryar gwamnatin hadin kan kasa, ya ce: “Babu wani wuri a kasar Libya, sai dai cibiyoyi na yau da kullum, ciki har da sojoji da ‘yan sanda,” Dbeibah, ya fadi haka ne biyo bayan al’amuran tsaro da suka faru a babban birnin kasar, Tripoli, a ranar litinin bayan kisan Abdul Ghani al-Kikli, wanda aka fi sani da “Ghaniwa,” kwamandan kungiyar da ake kira “Stability Support Apparatus”.

Bayanin na Dbeibah ya zo ne a yayin wani taron tsaro da aka gudanar a makon da ya gabata tare da mukaddashin ministan harkokin cikin gida, Imad al-Tarabulsi, karamin sakatare na ma’aikatar tsaro, Abdul Salam al-Zoubi, da daraktan sashen leken asiri na soji. Mahalarta taron sun ba da cikakken bayani kan matakan aiwatar da shirin tsaro na babban birnin kasar.

Dbeibah ya kara da cewa: “Dukkan sansanonin soji da kayayyakin aiki a kasar dole ne su kasance karkashin ma’aikatar tsaro da sojojin kasar Libya kadai,” yana mai jaddada cewa “babu wata kungiya da ke dauke da makamai a wajen wannan tsarin da ke da hakki, kuma horon hukumomin shi ne ka’idar da ba za a kebe kowa ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Halaka Sojojin Sahayoniyya Tare Da Jikkata Wasu A Beit Lahiya
  • Wasu Shugabannin Turai Sun Yi Barazanar Ladabtar Da Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza
  • Wata ‘Yar Jarida Ta Nuna Mamaki Kan Nuna Damuwa Da Ciwon Biden Maimakon Kisan Gillar ‘Yan Sahayoniyya
  • Fira Ministan Libiya Ya Tantance Bangarorin Da Kula Da Hakkin Tsaron Kasar Ya Rataya A Wuyarsu
  • Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri
  • Sojan Lebanon Daya Ya Jikkata Sanadiyyar Harin Sojan HKI Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Iran Ta Jaddada Kawo Karshen Bakar Siyasar gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Kan Al’ummar Falasdinu
  • Iran : Hare-haren da Isra’ila ta kai kan Yemen babban laifin yaki ne