Gwamnatin kasar Masar na shirin yin arangama ta soji da haramtacciyar kasar Isra’ila

Kafofin yada labaran Isra’ila, musamman tashar talabijin ta 14, sun watsa wani rahoto cewa: Gwamnatin kasar Masar na kokarin karfafa karfinta na soji a tsibirin Sinai, tana mai gargadin abin da ta bayyana a matsayin “yiwuwar rugujewar yarjejeniyar zaman lafiya” da aka rattaba hannu tsakanin kasashen biyu a shekara ta 1979.

Tashar talabijin ta NAN ta nakalto Eliyahu Dekel, tsohon shugaban hukumar leken asirin sojin haramtacciyar kasar Isra’ila kuma masani kan al’amuran Masar na cewa: Masar na cikin gaggawar shirin tunkarar rikicin soji, yana mai cewa “yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla tsakanin kasashen biyu a shekarar 1979 ta kasance cikin yanayi na rugujewa tun lokacin da aka rattaba hannu kan yarjejeniyar, kuma babu wata magana daya da ba a karya ba,” in ji shi.

A wata hira da aka yi da shi kan shirin na Oded Menashe, Dekel ya kara da cewa, nazarin hotunan tauraron dan adam ya nuna yadda ake gina filayen tashi da saukar jiragen sama na soja guda uku a yankin Sinai, baya ga gada da mashigar ruwa kusan 60 da ke kan mashigin Suez, yana mai bayyana hakan a matsayin wani yanayi na soji mai cike da damuwa.

Ya yi nuni da cewa, tun a shekara ta 2007, Masar ta kara kaimi kan ayyukan soji a yankin, wanda ya yi la’akari da shi a matsayin “shirin da take yi na yiyuwar arangama da sojojin mamayar Isra’ila.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza

Ministan yakin Isra’ila, Israel Katz, ya umarci sojojin kasar da su hana ayarin motocin agaji na arewacin Afirka shiga yankin Zirin Gaza da aka yi wa kawanya.

A cikin wata sanarwa ofishin Katz ya umarci sojojin Isra’ila da su hana “masu fafatuka daga Masar shiga yankin Zirin Gaza.

Katz bukaci “Hukumomin Masar dasu hana zuwan masu fafatukar a kan iyakar Masar da Isra’ila.”

Ministan ya ya bayyana hakan a matsayin hadari ga jami’an tsaron Isra’ila na IDF.”

Wannan dai na zuwa ne bayan ayarin motoci 100 da ya kunshi dubban masu fafatuka daga kasashen Morocco, Aljeriya, Tunisia, Libya da Masar, suka yunkuri anniyar wayar da kan al’ummar duniya kan matsalar jin kai a Gaza, da neman kawo karshen yakin kisan kare dangi, da karya shingen da Isra’ila ke yi da kuma kai muhimman kayayyakin jin kai a Gaza.

Ayarin da ya kunshi kungiyoyin kwadago da masu fafutukar kare hakkin bil’adama da ‘yan wasa da lauyoyi da likitoci da ‘yan jarida da na kungiyoyin matasa da dai sauransu ana sa ran za su shiga Masar a yau Alhamis kafin isa mashigar Rafah da ke kan iyaka a kudancin zirin Gaza.

Kafin hakan dama sojojin Isra’ila sun kwace jirgin ruwan agaji na Madleen da ke kan hanyarsa ta zuwa Gaza domin kai tallafi ga al’ummar Zirin, bayan shafe sama da watanni ashirin na yakin kisan kare dangi da Isra’ila ke yi.

An kama dukkan masu fafutukar na kasa da kasa su 12 da ke cikin jirgin, ciki har da mai fafutukar Sweden Greta Thunberg.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
  • Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa