Maniyatan Jigawa 550 Sun Isa Kasa Mai Tsaki Don Aikin Hajjin Bana
Published: 20th, May 2025 GMT
An dauke kashin farko na maniyyata 550 daga jihar jigawa zuwa Saudiyya a filin jirgin Nuhu Muhammadu Sunusi domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.
Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan jim kadan bayan tashinsu zuwa kasa mai tsarki.
Ya bayyana cewa maniyyatan sun fito ne daga kananan hukumomi 24 na jihar.
Ya ce kananan hukumomin sun hada da Kazaure, Roni, Gwiwa, Yankwashi, Gumel, Gagarawa, Garki, Maigatari, Suletankarkar, Babura, Jahun, da Miga.
Sauran sune Kafin Hausa, Auyo, Hadejia, Kirikasamma, Guri, Birniwa, Malam Madori, Dutse, Kiyawa, Ringim da Gwaram.
Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya yi nuni da cewa jirgin ya kuma kunshi wasu jami’an hukumar alhazai ta jiha da na likitoci da sauran masu ruwa da tsaki.
Ya bukace su da su kasance jakadu nagari na jiha da kasa baki daya yayin da suke kasa mai tsarki.
Labbo, ya yabawa jami’an tsaron jihar bisa yadda suka gudanar da aikin tantancewar a sansanin Hajji da filin jirgin sama.
Ya kuma yabawa gwamnan jihar Malam Umar Namadi bisa goyon baya da hadin kai da ake baiwa hukumar a kowane lokaci.
Shima da yake jawabi, Daraktan ayyuka na hukumar Alhaji Arab Sabo Aujara ya yi nuni da cewa, jihar ta yi wa maniyyata karfin gwiwa ta hanyar gayyato hukumomin gwamnatin tarayya da suka hada da hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA da shige da fice da kuma kwastam domin fadakar da mahajjatan abubuwan da za a dauka tare da sauran abubuwan da aka haramta.
Ya bukace su da su ji tsoron Allah a cikin ayyukansu yayin da suke kasa mai tsarki.
Arab ya kara da cewa, jihar ta tanadi komai don tabbatar da jin dadi da walwala a kasar ta Saudiyya
Wasu daga cikin mahajjatan da suka zanta da gidan rediyon Najeriya kafin tashin su, sun yabawa gwamnatin jihar da hukumar alhazai bisa yadda suka yi musu jinya a sansanin alhazai da filin jirgin sama.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, kamfanin jirgin Max Air ne ya dauke alhazan.
USMAN MZ
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600
Kamfanin kirar jiragen sama na kasar Sin wato AVIC ya ce ya cimma nasarar samar da jirgin sama dake iya tashi a kasa da ruwa irinsa na farko samfuri AG600 da aka yiwa lakabi da “Kun Long”. An kuma cimma nasarar gwajinsa a jiya Lahadi a birnin Zhuhai na lardin Guangdong.
Hakan ya nuna cewa, ingancin jirgin ya dace da ma’aunin da aka tanada, kuma ya alamta cewa jirgin samfuri AG600 ya samu iznin kira wato PC.
Rahotanni na cewa a ranar 20 ga watan Afrilun bana, jirgin samfurin AG600 ya samu takardar shaidar inganci ta samfurinsa, matakin da ya nuna cewa, nazarin da aka yi a wannan bangare ya cimma cikakkiyar nasara, kuma jirgin ya samu izinin shiga kasuwa. Kazalika, kamfanin AVIC zai gaggauta tabbatar da cewa “Kun Long”, ya taka rawa a fannin ba da agajin gaggawa, da tinkarar da kuma kandagarkin bala’u daga indallahi. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp