An dauke kashin farko na maniyyata 550 daga jihar jigawa zuwa Saudiyya a filin jirgin Nuhu Muhammadu Sunusi domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.

 

Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan jim kadan bayan tashinsu zuwa kasa mai tsarki.

 

Ya bayyana cewa maniyyatan sun fito ne daga kananan hukumomi 24 na jihar.

 

Ya ce kananan hukumomin sun hada da Kazaure, Roni, Gwiwa, Yankwashi, Gumel, Gagarawa, Garki, Maigatari, Suletankarkar, Babura, Jahun, da Miga.

 

Sauran sune Kafin Hausa, Auyo, Hadejia, Kirikasamma, Guri, Birniwa, Malam Madori, Dutse, Kiyawa, Ringim da Gwaram.

 

Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya yi nuni da cewa jirgin ya kuma kunshi wasu jami’an hukumar alhazai ta jiha da na likitoci da sauran masu ruwa da tsaki.

 

Ya bukace su da su kasance jakadu nagari na jiha da kasa baki daya yayin da suke kasa mai tsarki.

 

Labbo, ya yabawa jami’an tsaron jihar bisa yadda suka gudanar da aikin tantancewar a sansanin Hajji da filin jirgin sama.

 

Ya kuma yabawa gwamnan jihar Malam Umar Namadi bisa goyon baya da hadin kai da ake baiwa hukumar a kowane lokaci.

 

Shima da yake jawabi, Daraktan ayyuka na hukumar Alhaji Arab Sabo Aujara ya yi nuni da cewa, jihar ta yi wa maniyyata karfin gwiwa ta hanyar gayyato hukumomin gwamnatin tarayya da suka hada da hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA da shige da fice da kuma kwastam domin fadakar da mahajjatan abubuwan da za a dauka tare da sauran abubuwan da aka haramta.

 

Ya bukace su da su ji tsoron Allah a cikin ayyukansu yayin da suke kasa mai tsarki.

 

Arab ya kara da cewa, jihar ta tanadi komai don tabbatar da jin dadi da walwala a kasar ta Saudiyya

 

Wasu daga cikin mahajjatan da suka zanta da gidan rediyon Najeriya kafin tashin su, sun yabawa gwamnatin jihar da hukumar alhazai bisa yadda suka yi musu jinya a sansanin alhazai da filin jirgin sama.

 

Wakilinmu ya ruwaito cewa, kamfanin jirgin Max Air ne ya dauke alhazan.

 

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242

Hukumomi a India sun ce da yiwa a samu wanda ya tsira daga hatsarin jirgin samanAir India da ya faru a yau Alhamis.

Jirgin samfarin Boeing 787 Dreamliner wanda ya tashi Ahmedabad zuwa birnin Landan ya yi hatsari jim kadan bayan tashinsa dauke da fasinjoji 242 da ma’aikatan jirgin inji kamfanin air India.

Bayanan farko da kamfanin na Indiya ya fitar sun ce akwai, Indiyawa 169, ‘yan Burtaniya 53 da, ‘yan  Portugal 7 sai dan Canada guda a cikin jirgin. Kuma babu wanda ya tsira, a cewar shugaban ‘yan sandan Ahmedabad.

Hukumomin India da na Ingila da Portigal duk sun jajanta game da mummunan hatsarin.

Jami’an kashe gobara a arewa maso yammacin Indiya tun da farko sun shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa wani jirgin sama ya fado a filin jirgin.

Hotunan farko da aka watsa a gidajen talabijin na Indiya sun nuna wani jirgin sama yana shawagi a wata unguwa, kafin ya bace wurin ya turnuke da bakin hayaki.

Bayanai sun ce wannan shi ne hatsarin farko na jirgin Boeing 787 Dreamliner wanda ya fara aiki a shekarar 2011.

Kamfanin Boeing ya ce tuni ya fara tattara bayanai don sanin hakikanin abinda ya faru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa