An dauke kashin farko na maniyyata 550 daga jihar jigawa zuwa Saudiyya a filin jirgin Nuhu Muhammadu Sunusi domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.

 

Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana hakan jim kadan bayan tashinsu zuwa kasa mai tsarki.

 

Ya bayyana cewa maniyyatan sun fito ne daga kananan hukumomi 24 na jihar.

 

Ya ce kananan hukumomin sun hada da Kazaure, Roni, Gwiwa, Yankwashi, Gumel, Gagarawa, Garki, Maigatari, Suletankarkar, Babura, Jahun, da Miga.

 

Sauran sune Kafin Hausa, Auyo, Hadejia, Kirikasamma, Guri, Birniwa, Malam Madori, Dutse, Kiyawa, Ringim da Gwaram.

 

Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya yi nuni da cewa jirgin ya kuma kunshi wasu jami’an hukumar alhazai ta jiha da na likitoci da sauran masu ruwa da tsaki.

 

Ya bukace su da su kasance jakadu nagari na jiha da kasa baki daya yayin da suke kasa mai tsarki.

 

Labbo, ya yabawa jami’an tsaron jihar bisa yadda suka gudanar da aikin tantancewar a sansanin Hajji da filin jirgin sama.

 

Ya kuma yabawa gwamnan jihar Malam Umar Namadi bisa goyon baya da hadin kai da ake baiwa hukumar a kowane lokaci.

 

Shima da yake jawabi, Daraktan ayyuka na hukumar Alhaji Arab Sabo Aujara ya yi nuni da cewa, jihar ta yi wa maniyyata karfin gwiwa ta hanyar gayyato hukumomin gwamnatin tarayya da suka hada da hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA da shige da fice da kuma kwastam domin fadakar da mahajjatan abubuwan da za a dauka tare da sauran abubuwan da aka haramta.

 

Ya bukace su da su ji tsoron Allah a cikin ayyukansu yayin da suke kasa mai tsarki.

 

Arab ya kara da cewa, jihar ta tanadi komai don tabbatar da jin dadi da walwala a kasar ta Saudiyya

 

Wasu daga cikin mahajjatan da suka zanta da gidan rediyon Najeriya kafin tashin su, sun yabawa gwamnatin jihar da hukumar alhazai bisa yadda suka yi musu jinya a sansanin alhazai da filin jirgin sama.

 

Wakilinmu ya ruwaito cewa, kamfanin jirgin Max Air ne ya dauke alhazan.

 

USMAN MZ

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza.
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin