Aminiya:
2025-07-04@21:34:35 GMT

’Yan bindiga: Zamfara sun koma kwana a jeji

Published: 20th, May 2025 GMT

Mutane sun koma kwana a cikin jejin a sakamakon hare-haren ’yan bindiga a yankin Ƙaramar Hukumar Ƙaura Namoda da ke Jihar Zamfara.

Mazauna yankunan sukan dawo cikin gari su yini, idan dare ya yi kuma su shiga daji su kwana, sakamakon ƙaruwar hare-haren ’yan ta’adda, inda suka kashe mutum huɗu suka yi garkuwa da wasu 26.

Wani mazaunin Ƙauran Namoda da ya buƙaci a ɓoye sunansa ya ce adadin mutanen zai iya cin haka, inda ya tabbatar cewa maharan sun kashe wata mata tare da sace wasu 26.

Ya bayyana cewa daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su har da wani magidanci da matansa biyu da ’ya’yansa uku.

An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya An kama ɗan bindiga a hanyar zuwa aikin Hajji a Sakkwato

Wani ganau ya ce lamarin ya fi muni a ƙauyen Sabon Gari inda ’yan bindiga suka kashe wata mata sannan kuma yi garkuwa da wasu mutane sama da 20.

’Yan ta’addan sun tsananta kai hare-hare a kan ƙauyuka inda a Asabar da misalin karfe 1:30 suka kai hare-haren, duk kuwa da cewa an girke jami’an tsaro a garin Ƙaura Namoda.

Wata majiya a yankin ta ce ana zargin ’yan ta’addan suna da alaƙa da jagoran ’yan bindiga, Bello Ƙaura, wanda aka fi sani da Ɗan Sade, wanda ya ya addabi ƙananan hukumomin Ƙaura Namoda da Bunguɗu da kuma Maradun.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Ƙaura Namoda yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

An sa zare tsakanin ‘yan Kannywood da Alhikima

Tauraron Kannywood kuma mai sayar da maganin gargajiya, Abdullahi Alhikima ya magantu bayan da wasu ‘yan Kannywood suka caccake shi kan kalaman da ya yi a kansu.

Aminiya ta rawaito cewa hatsaniyar ta samo asali ne bayan fitattun ‘yan Kannywood da suka hada da Abdul M Sharif, Nura M Inuwa, Abubakar Bashir Maishadda, Sadik Sani Sadik, da sauransu suka kai wa tsohon dan takarar shugaban kasa a PDP Atiku Abubakar ziyarar goyon baya.

Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba

Wannan ya tunzura Alhikma kasancewar wasu daga cikin wadanda suka je mubayi’ar ‘ya’yan kungiyar YBN ne a baya, da kuma 13/13 ta ubangidansa, mawaki Rarara.

A cikin wadanda Alhikima ya caccaka har da Shugaban Hukumar Fina-finai ta Ƙasa, Ali Nuhu.

Sai dai a kan hakan ne kuma wasu ke hasashen lallai ta tabbata alaƙa ta yi tsami tsakanin Alin da Rarara, wadanda a da suke abokai.

To sai dai Alhikman ya yi mi’ara koma baya, inda a ranar Laraba ya fito yana bayar da haƙuri, a cikin wani bidiyo da ya karade soshiyal midiya.

“Ina amfani da wannan dama domin janye kalamaina, na kuma bayar da hakuri ga ‘yan masana’antar Kannywood. Na yi wasu maganganu kuma zan janye bisa dalilai guda uku.

“Na farko maganar da na yi wasu na ganin ciyaman Alhaji Dauda Kahutu Rarara shi ne ya saka ni na yi wannan maganar. Ina ba da hakuri domin barranta shi da ita, domin ni na yi ta. Domin ya kira ni ya kuma nuna min kuskuren da ke cikin maganganuna. Kuma dama cikar dan adam shi ne idan shugabanka ya ce ka yi daidai ka karbi daidai ne. Idan shugabanka ya ce kayi kuskure ka karba.

“Haka kuma akwai abokiyar aikina Aishatul Humaira ta zaunar da ni ta gwada min kurakuran da ke cikin maganar da na yi, musamman a kan mai girma MD, Ali Nuhu. Wanda uba ne a wurinta a masana’antar. Hallau a cikin masana’antar tana da aminai maza da mata wanda suke da alaka ta mutunci da mutunta juna.”

Sai dai Alhikma ya yi togaciya a ban hakurin nasa, in da ya ce iya ‘yan Kannywood zai bai wa hakuri ban da wadanda ya kira da ‘yan shisshigi’.

Ita ma dai Aishatul Humairan ta bai wa ‘yan Kannywood din hakuri duk da ba da yawunta Alhikima ya tayar da hazon ba,  musamman Ali Nuhu, wanda ta ce uba ne a gare ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
  • SON Ta Bada Shaidar Ingancin Kayayyaki Ga Wasu Kamfanoni A Kaduna
  • Filato: Mahara sun cire hannun matashi a kan hanyar komawa gida daga jana’iza
  • Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
  • ’Yan Majalisar Wakilai bakwai na Akwa Ibom sun koma APC
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • An sa zare tsakanin ‘yan Kannywood da Alhikima
  • Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
  • Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya
  • Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba