Aminiya:
2025-05-20@16:04:26 GMT

’Yan bindiga: Zamfara sun koma kwana a jeji

Published: 20th, May 2025 GMT

Mutane sun koma kwana a cikin jejin a sakamakon hare-haren ’yan bindiga a yankin Ƙaramar Hukumar Ƙaura Namoda da ke Jihar Zamfara.

Mazauna yankunan sukan dawo cikin gari su yini, idan dare ya yi kuma su shiga daji su kwana, sakamakon ƙaruwar hare-haren ’yan ta’adda, inda suka kashe mutum huɗu suka yi garkuwa da wasu 26.

Wani mazaunin Ƙauran Namoda da ya buƙaci a ɓoye sunansa ya ce adadin mutanen zai iya cin haka, inda ya tabbatar cewa maharan sun kashe wata mata tare da sace wasu 26.

Ya bayyana cewa daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su har da wani magidanci da matansa biyu da ’ya’yansa uku.

An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya An kama ɗan bindiga a hanyar zuwa aikin Hajji a Sakkwato

Wani ganau ya ce lamarin ya fi muni a ƙauyen Sabon Gari inda ’yan bindiga suka kashe wata mata sannan kuma yi garkuwa da wasu mutane sama da 20.

’Yan ta’addan sun tsananta kai hare-hare a kan ƙauyuka inda a Asabar da misalin karfe 1:30 suka kai hare-haren, duk kuwa da cewa an girke jami’an tsaro a garin Ƙaura Namoda.

Wata majiya a yankin ta ce ana zargin ’yan ta’addan suna da alaƙa da jagoran ’yan bindiga, Bello Ƙaura, wanda aka fi sani da Ɗan Sade, wanda ya ya addabi ƙananan hukumomin Ƙaura Namoda da Bunguɗu da kuma Maradun.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Ƙaura Namoda yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Faralin  

Sarkin Saudiyya, Salman Bin Abdulaziz, ya bayar da umarnin ɗaukar nauyin Hajjin iyalan Falasɗinawa 1,000 da suka rasa ‘yan uwansu sakamakon yaƙin da ke ci gaba da gudana a Zirin Gaza da Isra’ila.

Wannan taimako na cikin littafin kujerun Hajji da masarautar ke rabawa a kowace shekara ga al’umma ko kuma ɗaukar nauyin waɗanda suka cancanta, ciki har da waɗanda suka riga suka biya kuɗin Hajjin.

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

Sarkin ya bayyana wannan mataki ne a matsayin ɗaya daga cikin hanyoyin nuna goyon baya da jin ƙai ga al’ummar Falsɗinawa a wannan lokaci mai wahala da suke ciki sakamakon yaƙi da ƙasar Yahudawa ta Isra’ila ta ƙaddamar a Gaza.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hare-Haren Wuce Gona Da Irin Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3, sun sace 26 a ƙauyukan Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara
  • Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali
  • Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Faralin  
  • An kashe ’yan kasuwa 15 a wani sabon hari a Binuwai
  • Zubar Da Jini Mafi Muni A Cikin Daren Jiya A Zirin Gaza, Inda Falasdinawa 80 Suka Yi Shahada
  • Iran : Hare-haren da Isra’ila ta kai kan Yemen babban laifin yaki ne