Dalibai Makarantun Sakandare A Kwara Sun Karɓi Tallafin Karatu
Published: 20th, May 2025 GMT
Akalla dalibai marasa galihu 300 da ke makarantun gaba da sakandare daga zababbun al’ummomi a kananan hukumomin Edu/Patigi/Moro na jihar Kwara sun samu tallafin karatu don tallafa musu.
Da yake jawabi a wajen taron rabon tallafin karatu da aka gudanar a Ilorin, mai taken “Hatsarori na Shaye-shayen Miyagun Kwayoyi Tsakanin Dalibai A Manyan Makarantu” wanda Michael Imoudu tare da hadin gwiwar mamba mai wakiltar mazabar Edu/Moro/Patigi na Jihar Kwara, Ahmad Adamu -Saba ya shirya, ya ce za a yi rabon ne kashi biyu.
Dan majalisar wanda ya samu wakilcin mai taimaka masa, Muhammed Salihu, ya ce manufar shirin bayar da tallafin shi ne tallafawa daliban da iyayensu ba za su iya biyan wasu kudadensu a makaranta ba.
Saba ya bayyana cewa wasu ’yan gata da ke makaranta suma za su iya amfani da kudin wajen siyan littattafansu ko biyan kudin hayar gidansu .
Ya shawarci daliban da su tabbatar sun yi amfani da naira dubu dari da ake baiwa kowannen su domin manufar da aka sa a gaba.
Saba ta bukace su da su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi da sauran munanan dabi’u domin samun ingantacciyar rayuwa.
A nasa jawabin mukaddashin Darakta Janar Michael Imoudu National Institute For Labour Studies (MINILS), Fasto Ezekiel Ayorinde, wanda babban jami’in kula da harkokin kasuwanci na Cibiyar, Hassan Surajudeen ya wakilta, ya ce an raba tallafin ne da nufin inganta ilimin daliban.
Ya kuma shawarce su da su sanya kudin cikin hikima wajen neman ilimi.
A jawabansu daban daban wasu shugabannin al’umma a kananan hukumomin Moro/Edu/Patigi, Muhammed Aliyu Labas da Mohammed Baba (Shonga) sun yabawa mai gudanar da wannan karimcin.
Sun bukaci wadanda suka ci gajiyar kudin da su tabbatar sun yi amfani da kudin don manufar da ake son yi.
A cikin laccar sa mai taken “Hadarin Shaye-shayen Miyagun Kwayoyi A Tsakanin Dalibai A Manyan Makarantu” Babban Malamin, Abdullahi Galadima ya ce daga bayanan da ake da su matasa na da dabi’ar shiga shaye-shayen miyagun kwayoyi saboda matsin lamba na tsarawa da dai sauransu.
Ya shawarci matasa da su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi, su kuma yi karatun ta natsu domin kyautata rayuwarsu
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Karatu
এছাড়াও পড়ুন:
Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
Hukumar Kula da Yanayi (NiMet), ta sake fitar da gargaɗi game da yiwuwar ambaliyar ruwa a wasu jihohin a daminar bana.
A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, hukumar ta bayyana cewa Jihar Akwa Ibom ce ke fuskantar barazana mafi tsanani a halin yanzu.
Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a IranSauran jihohin da abin ka iya shafa sun haɗa da Sakkwato, Zamfara, Filato, Yobe, Bauchi, Bayelsa, Nasarawa, Binuwai, Ogun, Ekiti, Delta da kuma Ribas.
NiMet ta shawarci al’umma, musamman waɗanda ke zaune a cikin waɗannan jihohin, da su tabbatar sun yashe magudanan ruwa domin bai wa ruwa hanyar wucewa.
Haka kuma ta buƙaci mutane da su nisanci wuraren da ke da hatsarin ambaliya, kuma idan ruwa ya fara ƙarfi, su bar irin waɗannan wuraren domin kare lafiyarsu.
Ambaliya dai na daga cikin manyan matsalolin da ke janyo asarar rayuka da dukiyoyi a Najeriya a duk shekara.
A makonnin baya, garin Mokwa da ke Jihar Neja ya fuskanci ambaliya wadda ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 230.