HausaTv:
2025-07-11@07:35:09 GMT

Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna

Published: 15th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Tehran a shirye take ta shiga tattaunawa da kasashen Turai bisa mutunta juna.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, Araghchi da Ministan Harkokin Wajen Netherlands Caspar Veldkamp sun tattauna hanyoyin inganta alakar juna da sabbin abubuwa dake faruwa a yankin da na kasa da kasa.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya nanata tsarin kasar na kulla kyakkyawar alaka ta diflomasiyya da kasashen.

Iran da kasashen Turai dai na tattaunawar ba-zata kai a kai tun shekara ta 2021, shekaru uku bayan da Amurka ta fice daga yarjejeniyar nukiliyar iran – tare da maido da takunkumin da Washington ta kakaba wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

bangarorin kasashen Turai da suka shiga yarjejeniyar nukiliya – Birtaniya, Faransa da Jamus – sun kasa cika alkawarin da suka dauka na dawo da Washington cikin yarjejeniyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Tana Fatan HKI da Hamas Su Tsaida Budewa Juna Wuta Na Kwanaki 60 A Karshen Wannan makon

Jakadan Amurka na musamman a yankin yammacin Asiya Steven Witkoff  ya bayyana cewa yana fatan HKI da kuma kungiyar Hamas zasu cimma yarjeniyar tsagaita budewa juna wuta a karshen wannan makon.

Jakadan ya kara da cewa idan har yarjeniyar ta tabbata, kungiyar Hamas zata mikawa HKI yahudawa masu rai 10 da kuma gawakinn wasu 09 .

Steven Witkoff bai bayyana abinta ita Hamas da kuma sauran Falasdinawa zasu samu a wannan yarjeniyar na kwanaki 60 ba. Musamman bayan ta rasha falasdinawa kimani 57500 ya cikin watanni kimani 21 yahudawan suna fafatawa da ita ba.

Har’ila yau falasdinawa 150,000 suka ji rauni mafi yawansu mara da yara. A cikin wadanda aka kashe akwai yara kimani 12, 000

Daga karshe Witkoff, yace a halin yanzu sabani guda ne kacal ya rage ba’a warware ba, cikin guda hudu da ake tattaunawa da Hamas na lokaci mai tsawo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Limaman Turai Ta Nesanta Kanta Daga Wadanda Su Ka Ziyarci HKI
  • Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Iran Ta Musanta Neman Ci Gaba Da Gudanar Da Tattaunawa Da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Kazem Sajjadpour Ya ce: Iraniyawa Suna Daukan Tarayyar Turai Ma Goyon Bayan Harin Zaluncin Isra’ila Kansu
  • Amurka Tana Fatan HKI da Hamas Su Tsaida Budewa Juna Wuta Na Kwanaki 60 A Karshen Wannan makon
  • Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki
  • Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na  Sabuwar Tattaunawa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya