Aminiya:
2025-12-09@18:58:31 GMT

Kwamishinan Gombe ya rasu a hatsarin mota

Published: 25th, October 2025 GMT

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Gombe, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), ya rasu a hatsarin mota.

Gwamnatin Jihar Gombe ce, ta sanar da rasuwar cikin wata sanarwa da Daraktan Harkokin Watsa Labarai, Ismaila Uba Misilli, ya fitar a ranar Juma’a.

Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC Gwamnan Bauchi ya naɗa ɗan uwansa a matsayin sabon Sarkin Duguri

Sanarwar ta ruwaito cewa Bello ya rasu a kan hanyar Malam Sidi zuwa Gombe, bayan aukuwar wani mummunan hatsarin mota.

“Gwamnatin Jihar Gombe na cikin jimamin sanar da rasuwar Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Kanal Abdullahi Bello (mai ritaya), sakamakon a hatsarin mota da ya rutsa da shi a kan hanyar Malam Sidi zuwa Gombe,” in ji Misilli.

Sanarwar, ta bayyana cewa Bello ya rasu tare da wani jami’in ɗan sanda da ke tare da, Sajan Adamu Husaini.

Hatsarin ya rutsa da su yayin da suke dawowa daga Maiduguri, Jihar Borno, inda suka halarci wani taro na yankin Arewa Maso Gabas.

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana labarin rasuwar Kwamishinan a matsayin abun baƙin ciki.

Ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai biyayya, jajircewa da yi wa jama’a hidima, wanda ya nuna ƙwarewa wajen jagoranci da kishin ƙasa a ayyukansa a Gombe.

“Kanal Bello (mai ritaya) zai kasance abin koyi wajen biyayya, hidima ba tare da son kai ba.

“Ya gudanar da aikinsa da himma. Rashinsa babban giɓi ne ba wai ga iyalansa da gwamnatinmu ba, har ma da Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya,” in ji gwamnan.

Gwamnan ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, abokan aikinsa, da al’ummar Ƙaramar Hukumar Balanga.

Hakazalika, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan jami’in ɗan sandan da ya rasu tare da Kwamishinan.

Ya yi addu’ar Allah Ya gafarta musu tare da sanya su a Aljanna Firdausi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hatsarin mota Kwamishinan Tsaro rasuwa hatsarin mota Jihar Gombe

এছাড়াও পড়ুন:

ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Sakkwato (ASUU-SSU), ta zargi Mataimakin Shugaban Jami’ar (Vice-Chancellor) da kin bin umarnin Gwamnan Jihar Sakkwato game da sauke Bursar da ya kai lokacin ritaya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Sakkwato a ranar Litinin, 8 ga Disamba 2025, ƙungiyar ta ce Gwamna Dr. Ahmed Aliyu Sakkwato, wanda shi ne Visitor na Jami’ar, ya amince da buƙatarsu na tabbatar da bin dokokin Jami’ar ta hanyar amincewa da ritayar Bursar ɗin.

ASUU-SSU ta bayyana cewa Ofishin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar Sakkwato ya aika da takardar umarni mai lamba HS/ADM/101/VOL-1, ɗauke da kwanan wata 18 ga Nuwamba 2025, wadda ta umurci Bursar ya miƙa ragamar ofis ga jami’in da ya fi kowa girma a sashen Bursary, har sai an naɗa sabon Bursar bisa tanadin dokar Jami’ar Jihar Sakkwato ta 2009.

Sai dai ƙungiyar ta ce kusan wata guda ke nan VC ɗin bai aiwatar da umarnin ba.

Shugaban reshen ASUU-SSU, Kwamared Bello Musa, ya bayyana cewa sun rubuta wa VC takardar tunatarwa da wata takarda ta biyu, amma ba su samu amsa ba.

Haka kuma, sun gudanar da taro biyu da shi, amma ya dage cewa akwai wata amincewa da Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi ta jihar ta bayar a 2024 game da matsayin Bursar.

Sai dai ASUU ta ce wannan hujja “ba ta da tushe”, domin sabon umarnin Gwamna “ya fi ƙarfi kuma ya shafe duk wani tsohon matsayi”, musamman ma ganin cewa Bursar ya kai lokacin ritaya tun 3 ga Oktoba 2024.

A cewarta, Ma’aikatar Kula Da Ma’aikata ta riga ta aika masa da takardar ritaya ta hannun Ma’aikatar Kudi ta jihar.

Ƙungiyar ta ce ci gaba da bari tsohon ma’aikaci ya rattaɓa hannu kan muhimman takardun Jami’a “na karya doka, kuma na tauye ikon Jami’a (University Autonomy).”

ASUU-SSU ta yaba wa Gwamnan jihar bisa “ƙarin nuna biyayya ga doka da buɗe ƙofar sauraron ƙorafe-ƙorafe”, tare da buƙatar ya tabbatar da cewa ba a katse hanyoyin isar da sahihan koke-koke zuwa gare shi ba.

Ƙungiyar ta ce zanga-zangar lumana da ta gudanar a Jami’ar na nufin matsa wa VC lamba ya aiwatar da umarnin Gwamna ba tare da ɓata lokaci ba, domin tabbatar da zaman lafiya da daidaiton aiki.

Ta kuma sha alwashin ɗaukar “mataki mafi tsauri” idan ba a aiwatar da umarnin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • An kama tsohon fursuna ya je fashi da bindiga AK-47
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano
  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161