Aminiya:
2025-12-05@07:38:52 GMT

APC ta rage wa Mata kuɗin tsayawa takara a Borno

Published: 20th, October 2025 GMT

Jam’iyyar APC reshen Jihar Borno ta rage wa mata kashi 50 cikin 100 na farashin fom ɗin tsayawa takara, makonni gabanin zaɓen kananan hukumomi da za a gudanar a ranar 13 ga Disamba, 2025.

Da yake sanar da hakan a Maiduguri, shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Bello Ayuba, ya ce an ɗauki matakin ne domin magance matsalar ƙarancin kuɗi da ke hana mata shiga siyasa da tsayawa takara.

Yadda Morocco ta kafa tarihin ɗaga Kofin Duniya na FIFA U20 Dembele ya dawo PSG bayan jinyar makonni

“Wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarin da muke yi na samar da daidaito ga mata a fagen siyasa.

“Muna son ganin mata da yawa suna jagoranci a matakin ƙasa, suna ba da gudummawa da ƙarfinsu wajen gudanar da mulki,” in ji Ayuba.

A cewarsa, “an ƙayyade farashin fom ɗin neman kujerar shugaban ƙaramar hukuma ga maza kan naira miliyan 2, yayin da fom ɗin kansila zai ci ₦500,000, amma mata za su biya rabin wannan adadi — ₦1 miliyan da ₦250,000.”

Ya ƙara da cewa an kafa kwamitocin tantancewa da sasantawa domin tabbatar da cewa zaɓen fidda gwani zai gudana cikin gaskiya da lumana a dukkan ƙananan hukumomi 27 da gundumomi 112 na jihar.

“Za a gudanar da zaɓen fidda gwani a lokaci guda a ƙarshen wannan watan domin guje wa maguɗin zaɓe,” in ji shi.

Ayuba ya jaddada aniyar jam’iyyar ta tabbatar da sahihin zaɓe, inda ya ce Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Borno (BOSIEC) za ta gudanar da babban zaɓen a ranar 13 ga Disamba, 2025.

“Mun himmatu wajen tabbatar da ɗorewar dimokuraɗiyya ta hanyar adalci, daidaiton jinsi, da kuma gudanar da zaɓe cikin lumana,” in ji shi.

“Mata na da matuƙar muhimmanci ga shugabanci, kuma wakilcinsu yana ƙarfafa tsarin mulki.”

Masu sa ido da ƙungiyoyin kare haƙƙin mata sun yaba da matakin jam’iyyar APC, inda suka bayyana shi a matsayin muhimmiyar hanya ta ƙara daidaiton jinsi a siyasar Jihar Borno.

Sun ce rage kuɗin fom ɗin tsayawa takara ga mata ba kawai zai ƙarfafa gwiwar mata masu neman tsayawa takara ba, har ma zai zaburar da ƙananan ‘yan mata su ga shugabanci a matsayin abin da za su iya cimma.

Wannan mataki dai ya yi daidai da kiraye-kirayen ƙasa da ƙasa na ƙara shigar da mata cikin harkokin mulki, tare da ƙarfafa imanin cewa dimokuraɗiyya na bunƙasa ne idan maza da mata suka haɗa kai wajen tsara makomar al’ummarsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Borno Siyasa tsayawa takara

এছাড়াও পড়ুন:

An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna

Fargaba ta lulluɓe al’ummar Ungwan Nungu da ke gundumar Bokana a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna, bayan wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da mazauna yankin 11 a ranar Asabar yayin da suke dawowa daga gonakinsu.

Mazauna yankin sun ce an tare mutanen ne a wata hanyar daji da ke kusa da unguwar da yamma, inda aka tafi da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Lamarin ya tayar da hankula a ƙauyukan da ke kewaye, inda iyalai da dama suka kwana cikin fargaba.

Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu cewa wasu daga cikin waɗanda aka sace matasa ne da suka tafi gona domin yin roron wake lokacin da aka afka musu.

NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa

Ya ce: “An fara kai hari ne ga mutane 15, wasu sun tsere, wasu kuma aka sake su ba tare da sharaɗi ba. Amma har yanzu mutum 11 suna hannun ’yan bindiga, kuma sun buƙaci a biya su kuɗin fansa na naira miliyan biyar,” in ji shi.

Da yake tabbatar da afkuwar lamarin cikin wata sanarwa a ranar Talata, ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazavar Jama’a/Sanga, Hon. Daniel Amos, ya bayyana satar mutanen a matsayin mugunta da rashin tausayi, tare da yin Allah-wadai da kai hari kan talakawa masu aikin halaliya.

“Muna buƙatar kara tsaurara tsaro, yin amfani da dabarun bayanan sirri, da ɗaukar matakan gaggawa da haɗin gwiwa domin kwantar da hankalin jama’a da kuma ceto waxa0nda aka sace,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata
  • Rundunar Ruwa ta IRGC na Gudanar Da Atisayen Soja a Tekun Fasha
  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • Jagora: Musulunci Ya Daukaka Mata Matukar Dauka
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna