Aminiya:
2025-10-23@11:18:34 GMT

’Yan uwana 8 sun rasu a fashewar tanka a Neja — Wani Mutum

Published: 23rd, October 2025 GMT

Wani mutum mai suna Mallam Surajo Muhammad Shehu ya rasa ’yan uwansa takwas, lokacin da tankar mai ta yi bindiga a garin Essa da ke kan hanyar Agaie zuwa Bida, a Jihar Neja.

Lamarin ya auku a ranar Talata, wanda aƙalla mutum 28 ciki har da mata da ƙanana yara, suka rasa rayukansu lokacin da tankar ta kife kuma ta kama da wuta yayin da jama’a ke ƙoƙarin ɗibar mai.

Tun da PDP ta bar mulkin Najeriya maguɗin zaɓe ya ragu – Akpabio Dangote zai sayar da kaso 10 na hannun jarin matatar man shi

Wasu da dama sun ji rauni kuma an garzaya da su Asibitin Gwamnatin Tarayya (FMC) da ke Bida.

Shehu, ya ce mata ne suka fi mtuuwa saboda maza sun tafi gona lokacin da lamarin ya faru.

Ya zargi mazauna yankin da ƙin bin gargaɗin da aka sha yi musu kan hatsarin ɗibar mai daga tankar da ta kife.

Hakimin Essa, Alhaji Adamu Bagudu, ya tabbatar da cewa an binne mutum 28, ciki har da mata 24.

Ya ce an sha gargaɗin jama’a kan hatsarin wannan ɗabi’a, amma talauci da wahalar rayuwa ya sa mutane yin watsi da igargaɗin

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), ta ce aƙalla mutum 80 lamarin ya shafa, inda aka kai wasu 17 Abuja domin samun kulawa ta musamman.

Gwamnan Gombe kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Inuwa Yahaya, ya bayyana alhininsa kan lamarin tare da kiran gwamnati da ta ƙara tsaurara matakan tsaro da kuma gyaran hanyoyi.

Majalisar Wakilai ta Ƙasa ta kuma roƙi Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta gyara hanyar Bida zuwa Agaie wadda ke janyo salwantar rayukan mutane.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hatsari tankar mai yara

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

Sun ce wadanda suka mutu yawancinsu wadanda suka je kwaso man fetur ne a lokacin da tankar ta yi hatsari kafin fashewar.

 

Shugabannin Direbobin Tankar Mai na Jihar Neja (PTD) da Kungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Gas ta Nijeriya (NUPENG) ta kasa, Kwamared Farouk Mohammed Kawo, sun tabbatar wa LEADERSHIP faruwar lamarin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba October 21, 2025 Manyan Labarai NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi  October 21, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu October 21, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DSS ta cafke mutum 3 kan zargin sayar wa ’yan bindiga makamai a Kaduna
  • Gwamnatin Tarayya ta yi jimami kan mutuwar mutanen da suka rasu a fashewar motar mai a Jihar Neja
  • Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 
  • Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja
  • Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a fashewar tanka a Neja
  • Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
  • Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja
  • Fashewar tankar mai ta yi ajalin mutum 30 a Neja
  • Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja