’Yan uwana 8 sun rasu a fashewar tanka a Neja — Wani Mutum
Published: 23rd, October 2025 GMT
Wani mutum mai suna Mallam Surajo Muhammad Shehu ya rasa ’yan uwansa takwas, lokacin da tankar mai ta yi bindiga a garin Essa da ke kan hanyar Agaie zuwa Bida, a Jihar Neja.
Lamarin ya auku a ranar Talata, wanda aƙalla mutum 28 ciki har da mata da ƙanana yara, suka rasa rayukansu lokacin da tankar ta kife kuma ta kama da wuta yayin da jama’a ke ƙoƙarin ɗibar mai.
Wasu da dama sun ji rauni kuma an garzaya da su Asibitin Gwamnatin Tarayya (FMC) da ke Bida.
Shehu, ya ce mata ne suka fi mtuuwa saboda maza sun tafi gona lokacin da lamarin ya faru.
Ya zargi mazauna yankin da ƙin bin gargaɗin da aka sha yi musu kan hatsarin ɗibar mai daga tankar da ta kife.
Hakimin Essa, Alhaji Adamu Bagudu, ya tabbatar da cewa an binne mutum 28, ciki har da mata 24.
Ya ce an sha gargaɗin jama’a kan hatsarin wannan ɗabi’a, amma talauci da wahalar rayuwa ya sa mutane yin watsi da igargaɗin
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), ta ce aƙalla mutum 80 lamarin ya shafa, inda aka kai wasu 17 Abuja domin samun kulawa ta musamman.
Gwamnan Gombe kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Inuwa Yahaya, ya bayyana alhininsa kan lamarin tare da kiran gwamnati da ta ƙara tsaurara matakan tsaro da kuma gyaran hanyoyi.
Majalisar Wakilai ta Ƙasa ta kuma roƙi Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta gyara hanyar Bida zuwa Agaie wadda ke janyo salwantar rayukan mutane.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hatsari tankar mai yara
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, tare da haɗin gwiwar maharba, sun samu nasarar tarwatsa gungun masu garkuwa da mutane, tare da kama mutum bakwai da ake zargi da aikata laifuka a Jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da Adamawa.
Rundunar ta samu nasarar ne bayan kama Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40 daga ƙauyen Tilde a Funakaye, a ranar 23 ga watan Nuwamba 2025.
An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan KwaraAn kama shi ne bayan samun bayanan sirri kan hulɗa da masu satar shanu.
Abdullahi, ya amsa cewa yana da hannu a garkuwa da mutane tare da bayyana sunayen waɗanda suke aikata laifin tare.
A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, jami’an Operation Hattara tare da maharba ne suka kai samame maɓoyarsu a ranar 28 ga watan Nuwamba 2025, inda suka kama mutum shida bayan yin artabu.
Waɗanda aka kama sun haɗa da; Usman Mohammed, Hussain Idris, Adamu Tukur, Ya’u Abdullahi, Ali Umar, Hassan Usman da Abdullahi Ibrahim.
Rundunar ta ce waɗanda ake zargin sun amsa cewa suna da hannu a garkuwa da mutane tare karɓar kuɗin fansa kusan Naira miliyan 150.
Jami’an sun shiga dajin Gadam, inda suka samu bindiga ƙirar GPMG mai jigida guda ɗaya da harsasai takwas bayan wata musayar wuta da suka yi wasu ’yan ta’adda da suka tsere.
Haka kuma an gano suna da hannu wajen garkuwa da wani mutum a ƙauyen Barderi a Akko, a ranar 15 ga watan Janairun 2025.
Sun tsare mutumin na tsawon makonni biyu kafin karɓar Naira miliyan 15 a matsayin kuɗin fansa.
DSP Buhari, ya ce ana cigaba da bincike, kuma za a gurfanar da su a kotu.
Ya roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa rundunar sahihan bayanai domin inganta harkokin tsaro.
Rundunar ‘Yan Sandan Gombe ta ce za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.