Aminiya:
2025-12-06@08:58:44 GMT

Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya

Published: 22nd, October 2025 GMT

Wasu da ake zargin masu kwacen waya ne sun kashe ma’aikaciyar jinya a Asibitin Gambo Sawaba da ke Zariya a jihar Kaduna mai suna Hadiza Musa.

Bayanai sun ce marigayiyar it ace mataimakiyar shugabar sashen haihuwa a asibitin.

Majalisa ta soma binciken yadda aka kashe $4.6bn na tallafin kiwon lafiya Gwamna Bala Mohammed ya ƙirƙiri sabbin masarautu 13 a Bauchi

Mijinta, Hamza Ibrahim Idris, wanda ke aiki a Abuja, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an kashe matarsa ne a ranar Asabar yayin da take dawowa daga aiki.

“A ranar Asabar, ta kira ni ta ce za ta je wajen gyaran gashi sannan ta ziyarci wani shagon masu magani a Filin Mallawa, Tudun Wada Zariya, kuma na amince.”

“Bayan na tura mata kudi, kiranmu na ƙarshe shi ne lokacin da ta bar wajen sayar da maganin kusan ƙarfe 6 na yamma. Daga nan ban sake samun ta ba.”

“Na ci gaba da kiranta har zuwa safiyar ranar Lahadi, sai na ɗauka cajin wayarta ne ya ƙare.”

Idris, wanda ya farfado daga suma a ranar Talata bayan girgizar da lamarin ya haifar, ya ce daga baya ya gano cewa marigayiyar ta hau babur din haya kusan ƙarfe 6:30 na yamma a ranar Asabar, amma daga bisani wasu suka kai mata hari don su kwace wayarta.

“Alamu sun nuna matse hannayenta aka yi, alamar cewa an tilasta mata yayin da ake ƙoƙarin kwace wayar.”

“Sannan an bugi kanta da ƙarfi, inda jini ya taru a kan nata, wanda nake zaton shine ya jawo mutuwarta.”

Idris ya ce bayan ta suma, sai barayin suka sace wayarta suka jefar da ita a gefen titi kusa da filin Idi na Mallawa a Tudun Wada Zariya.

Ya ce wani mai tausayi da ya same ta ya garzaya da ita zuwa wani asibiti, daga bisani aka tura ta zuwa Asibitin Koyarwa na ABU, Shika, inda aka tabbatar da rasuwarta.

Mijinta ya ce Hadiza ta rasu watanni uku bayan rasuwar ’yar uwarta, wadda ta ɗauki ‘ya’yanta uku a matsayin nata.

“Ta bar ‘ya’yanta uku da kuma waɗanda ta ɗauka bayan rasuwar ’yar uwarta.”

A nasa bangaren, Sakataren Asibitin, Abdulkadir Balele Wali, ya ce Hadiza mataimakiyar shugabar sashen haihuwa ce, kuma ta halarci aiki a ranar Juma’a har zuwa yamma.

Ya bayyana ta a matsayin kwararriya, mai himma da sadaukarwa, wadda ta ba da gudunmawa wajen ceton rayukan jama’a.

Sakataren ya ce rasuwarta babban rashi ne ga asibitin gaba ɗaya.

Mansur Hassan, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sanda a Kaduna, bai samu daga wayar wakilinmu ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwacen waya Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran

Kamfanonin jiragen sama kasashen yamma sun bukaci Amurka ta basu izinin ratsawa ko zuwa kasar Iran bayan dakatarwa saboda yakin kwanaki 12 a cikin watan yunin da ya gabata.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto wasu majiyoyin gwamnatin Amurka na fadar cewa a halin yanzu babu wata barazana ta sake komawa yaki da kasar Iran. Sannan jita-jitan da wasu kafafen yada labarai suke yadawa dange da sake komawa yaki da kasar Iran ba gaskiya bane. A cikin yan makonnin da suka gabata ne wasu kamfanonin jiragen saman fasinja na kasashen yamma suka farfado da zirga-zirga zuwa kasar Iran bayan bayan fara yakin watan yuni

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI December 3, 2025 An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci December 3, 2025 Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu December 3, 2025 Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza December 3, 2025 Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta December 3, 2025 Kasar Qatar Ta Gargadi Isra’ila Game Da ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza December 3, 2025 Sharhi: HKI tana fama da karancin sojoji a dukkan rassan sojojin kasar December 2, 2025 Shugaba Pizishkiyan:  Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufa December 2, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Janar Chiristopher Musa ( Ritaya) A Matsayin Ministan Tsaro December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata
  • MDD ta bukaci a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma janyewa daga Tuddan Golan na Siriya
  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi
  • Jagora: Musulunci Ya Daukaka Mata Matukar Dauka
  • Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina