Red Cross ta kafa cibiyoyin rage haɗurran bala’o’i a makarantun Gombe
Published: 20th, October 2025 GMT
Ƙungiyar Agaji ta Red Cross ta Najeriya (NRCS), tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Italiya, ta kafa cibiyoyin Rage Haɗurran Bala’o’i (Disaster Risk Reduction – DRR) a makarantun sakandare guda biyu a Jihar Gombe, domin inganta shirye-shiryen kare kai daga bala’o’i da kuma ƙarfafa juriya a tsakanin matasa.
Makarantun da suka amfana da wannan shiri su ne Ƙaramar Sakandaren Gwamnati ta Pilot da kuma Sakandaren Gwamnati ta Comprehensive, Deba.
NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU An maka mahaifi a kotu kan cefanar da gidan ɗansa a KanoA yayin bikin ƙaddamar da cibiyoyin, ƙungiyar Red Cross ta raba kayan karatu da suka haɗa da jakunkuna masu ɗauke da bayanai kan DRR, littattafan rubutu, alƙalumma da kayan lissafi ga dalibai, domin ƙara musu ilimi da shiri na kare kai daga haɗurra.
Sakataren Red Cross reshen Jihar Gombe, Murtala Aji Alliyu, ya bayyana cewa manufar wannan shiri ita ce “kama su tun suna ƙanana,” ta hanyar koya musu ilimi mai amfani a fannoni huɗu — wato tsaftar muhalli, bayar da agajin gaggawa, yada bayanai, da kuma shirye-shiryen kare kai daga bala’o’i.
Ya ce ana aiwatar da wannan shiri a jihohi 12 na Najeriya domin rage haɗarin bala’o’i da kuma ƙarfafa tsaron al’umma ta hanyar ilmantar da matasa tun daga makaranta.
“Manufar ita ce a shirya matasa su san yadda za su kare kansu da kuma yadda za su amsa idan wata gaggawa ta faru. Idan aka ba su ilimi, za su zama jakadun sauyi da za su taimaka wajen gina al’umma mai juriya da tsaro,” in ji Alliyu.
A nasa jawabin, wanda ya wakilci Sarkin Deba, Alhaji (Dr) Ahmad Usman, wato Hakimin Bokna, Alhaji Abubakar Usman Tafidan Deba, ya yaba wa Red Cross da Gwamnatin Italiya bisa wannan shiri da ya bayyana a matsayin mai matuƙar amfani.
Ya buƙaci dalibai su ɗauki shirin da muhimmanci tare da haɗa gwiwa da malamansu domin tabbatar da ɗorewarsa.
Mataimakiyar Shugabar Makarantar Gwamnati ta Pilot, Malama Salifatu Abubakar, wacce ta wakilci shugaban makarantar, ta gode wa Red Cross bisa wannan kyakkyawan aiki, tare da kira ga ɗalibai da su yi amfani da ilimin da aka koya musu yadda ya kamata.
Ta ce wannan shiri ba wai ɗaliban kawai zai amfanar ba, har ma zai taimaka wajen yaɗa ilimin kare kai daga bala’o’i da kuma tabbatar da tsaro a faɗin Jihar Gombe.
Wasu daga cikin malamai da ɗalibai sun nuna farin ciki da wannan shiri, inda suka bayyana shi a matsayin abin da ya zo a kan kari kuma mai tasiri sosai.
Sun kuma yi kira ga sauran ƙungiyoyin agaji da na ci gaba da su yi koyi da Red Cross wajen aiwatar da shirye-shiryen da za su taimaka wajen gina al’umma mai juriya da kwanciyar hankali.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliya jihar Gombe kare kai daga wannan shiri
এছাড়াও পড়ুন:
MDD ta bukaci a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma janyewa daga Tuddan Golan na Siriya
Babban taron Majalisar Dinkin Duniya ya amince da wasu kudurori guda biyu da ke kira da a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma Tuddan Golan na Siriya.
Djibouti, Jordan, Mauritania, Qatar, Senegal, da Falasdinu ne suka gabatar da daftarin kuduri game da Falasdinu.
Kasashe 151 ne suka kada kuri’a a kan hakan, yayin da kasashe 11, ciki har da Amurka, suka ki amincewa da hakan, sai kuma wasu 11 da suka ce ba ruwansu.
Kudirin da aka amince da shi ya sake tabbatar da alhakin Majalisar Dinkin Duniya game da batun Falasdinu tare da yin kira da a kawo ƙarshen mamayar Isra’ila a yankunan da aka mamaye tun 1967, yayin da yake goyon bayan samar da kasashe guda biyu a matsayin mafita.
Babban taron ya kuma amince da wani kuduri, wanda Masar ta gabatar, yana kira ga Isra’ila da ta janye daga Tuddan Golan na Siriya tare da bayyana mamayar a matsayin haramtacce.
An amince da kudurin da kuri’u 123, sai 7 da suka ki, da kuma 41 da suka ce akai kasuwa. Amurka tana cikin waɗanda suka yi adawa da shi.
Wannan kuduri ya bayyana cewa mamaye da kuma kwace Golan da Isra’ila ta yi ya saba wa kuduri mai lamba 497 na Majalisar Tsaro, wanda aka amince da shi a shekarar 1981. A cikin sharhin farko da ta yi bayan amincewa da kudurin, Ma’aikatar Harkokin Wajen Siriya ta bayyana cewa “tana kira ga Isra’ila da ta janye daga dukkan tuddan Golan da ta mamaye.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe December 4, 2025 Rundunar Ruwa ta IRGC na Gudanar Da Atisayen Soja a Tekun Fasha December 4, 2025 Dan wasan Taekwando Na kasar Iran Ya Samua Lambar Yabo Ta Zinariya December 4, 2025 Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Gaza December 4, 2025 Iran: Tsaron Yankin Tekun Fasha Jan Layi Ne Da Za’a Fuskanci Mayar Da Martani Adan Aka Taba Shi December 4, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Dan Adam Sun Kira Ga Kasar Kanada Ta Kama Olmert Da Livni December 4, 2025 Majalisa Ta Tabbatar Da Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro December 4, 2025 Jagora: Musulunci Ya Daukaka Mata Matukar Dauka December 3, 2025 MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI December 3, 2025 An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela December 3, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci