Aminiya:
2025-10-24@18:23:55 GMT

Tinubu ya sauke hafsoshin tsaro, ya maye gurbinsu da wasu

Published: 24th, October 2025 GMT

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sauke Janar Christopher Musa daga mukaminsa na Babban Hafsan Tsaron Kasa.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sunday Dare, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, ya fitar a ranar Jumma’a.

An kama Sakataren APC na mazaba a Yobe kan zargin aikata kisan kai Gwamnonin PDP na yanzu za su rusa mana jam’iyya — Wike

A cewar sanarwar, an nada Janar Olufemi Oluyede, wanda shi ne Shugaban Sojin Ƙasa, a matsayin Sabon Babban Hafsan Tsaron Ƙasa.

An kuma naɗa Manjo Janar W. Shaibu a matsayin Shugaban Sojin Ƙasa, Air Vice Marshal S.K. Aneke a matsayin Shugaban Rundunar Sojin Sama, da Rear Admiral I. Abbas a matsayin Shugaban Rundunar Sojin Ruwa.

Manjo Janar E.A.P. Undiendeye, wanda shi ne Shugaban Sashen Leken Asirin Tsaro (Defence Intelligence), zai ci gaba da rike mukaminsa.

Sanarwar ta bayyana cewa wannan sauyi na cikin shirin gwamnati na inganta tsaron a Najeriya.

Shugaba Tinubu, ya gode wa tsohon Babban Hafsan Tsaron ƙasa, Janar Christopher Musa, da sauran tsoffin hafsoshi bisa gudunmawa da jagorancin da suka yi.

Ya kuma bukaci sabbin hafsoshin da su nuna ƙwarewa, jajircewa, da haɗin kai domin inganta tsaro a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban Hafsan Tsaro Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

 

Sanarwar da aka fitar a karshen taron ta bayyana cewa, matakin na daga cikin kokarin da ake yi na karfafa hadin kan jam’iyyar da tabbatar da daidaiton wakilcin yanki a cikin tsarin shugabancin jam’iyyar PDP.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja  October 23, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas October 23, 2025 Labarai NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa October 23, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya
  • Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, Ta Kaddamar da Dakin Karatu Na Zamani a Zamfara
  • Majalisar Tattalin Arziki Ta Amince da Shirin Gyara Cibiyoyin Horar da Jami’an Tsaro
  • Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027
  • Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
  • Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa
  • ISWAP: Mun kawar da duk wata barazana — Gwamnatin Ondo
  • Mai Ba Da Shawara Kan Harkokin Tsaron Iraki Ya Gana Da Hafsan Hafsoshin Sojojin Kasar Iran
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni