Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa  zata kara karfafa dankon zumunta da Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa NAFDAC.

Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin da mahukunta hukumar NAFDAC suka ziyarce shi a ofishin sa dake Dutse babban birnin jihar.

Ya bayyana farin cikinsa da ziyayar, inda ya jaddada bukatar aiki tare domin cimma dukkan nasarar da ake bukata a tsakanin hukumomin biyu.

Da yake bayani dangane da shirin da hukumar alhazan take yi, Labbo yace dukkanin shirye-shirye sunyi nisa na rigistar kujerun aikin hajji shekarar 2026.

Yana mai cewar, hukumar NAFDAC tana cikin masu ruwa da tsaki na hukumar jin dadin alhazan jihar.

Alhaji Ahmed Labbo, yayi nuni da cewar akowane lokaci za’a iya bukatar tattauna muhimman bayanai na shirye-shiryen aikin hajji domin bada ta su gudunmuwar.

Tun farko a jawabin sa, sabon Shugaban hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC a jihar jigawa, Alhaji Mansur Muhammad yace makasudin ziyarar shi ne domin gabatarwa gami da neman goyan bayan hukumar jin dadin alhazan ta jihar.

Ya kara da cewar, hukumar tana daga cikin hukumomi dake aiki tare da hukumar NAFDAC musamman a lokacin fara jigilar maniyyata.

Mansur Muhammad yace za su ci gaba da bai wa hukumar cikakken hadin kai da goyan baya a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Bisa kididdigar da hukumar kula da kudaden kasashen waje ta kasar Sin ta gabatar a yau ranar 22 ga wannan wata, a watan Satumba, yawan kudin da aka yi hada-hadarsu ta fuskar samun kudin shiga da kuma wadanda aka kashe na kamfanoni da daidaikun mutane da sauran hukumomin da ba na banki ba na kasar Sin ya kai dalar Amurka triliyan 1.37, wanda ya karu da kashi 7 cikin dari bisa na watan Agusta. Yawan kudin shiga da na kashewa da ya shafi kudaden kasashen waje na kasar Sin a farkon rabu’i na uku na bana ya kai dalar Amurka triliyan 11.6, wanda ya kai matsayin koli a tarihi, kana ya karu da kashi 10.5 cikin dari bisa na makamancin lokacin bara.

Mataimakin shugaban hukumar kuma kakakin hukumar Li Bin ya bayyana cewa, kasar Sin ta kiyaye samun karuwar cinikin waje, yawan kudin shiga a fannin cinikin kaya ya ci gaba da samun karuwa, kana an kiyaye samun hada-hadar kudi a fannonin samar da hidimomi da zuba jari a tsakanin kasa da kasa.

Li Bin ya bayyana cewa, tun daga farkon bana, an tafiyar da kasuwar kudaden waje ta kasar Sin yadda ya kamata yayin da ake fuskantar yanayi na rashin tabbas a kasashen waje, kuma an kiyaye kyakkyawan zaton yadda kasuwa za ta kasance, da tabbatar da yanayin hada-hadar kudaden waje, inda hakan ya shaida karfin kasar Sin a wannan fanni. (Zainab Zhang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera October 22, 2025 Daga Birnin Sin Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana October 22, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli October 22, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano
  • DSS ta cafke mutum 3 kan zargin sayar wa ’yan bindiga makamai a Kaduna
  • Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11
  • Jerin ’yan wasan da ke takarar lashe kyautar gwarzon Afirka na bana
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Sanar Da Wa’adin Biyan Kafin Alkalami Na Shekarar 2026
  • UNICEF Ya Tabbatar Da Anniyar Na Karfafa Jagorancin Mata A Fannin Ilimi
  • Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 2 Wajen Binciken Albarkatun Kasa
  • Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo
  • Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Biliyan Daya Wajen Gyaran Ajujuwa A Makarantu