Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada cewa yaki da matsalar rashin tsaro a jihar nauyi ne na  gwamnatinsa da sauran masu ruwa da tsaki, da ma al’umma baki.

Wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a ranar Litinin, ta ce gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da yake jagorantar taron majalisar zartarwa ta jihar karo na 18 da aka gudanar a fadar gwamnati da ke Gusau.

Sanarwar ta ce, majalisar ta tattauna kan muhimman batutuwa da suka shafi jihar, ciki har da tsaro, ilimi, kiwon lafiya, da cigaban ayyukan raya kasa.

Dr. Lawal ya tunatar da mambobin majalisar muhimmancin hadin kan su wajen yaki da rashin tsaro a karkashin wannan gwamnati.

“Muna samun gagarumin ci gaba wajen dawo da zaman lafiya a mafi yawan sassan jihar. An raunana karfin ‘yan bindiga fiye da yadda ake gani a baya,” in ji shi.

Ya bukaci mambobin majalisar su kasance masu saurin daukar mataki, tare da kusanci da al’ummarsu da zababbun shugabannin kananan hukumomi, da kuma ci gaba da bayar da rahoton halin tsaro ga Kwamishinan Tsaro na Jihar.

“Haka kuma, mu ci gaba da addu’a domin shahidanmu da suka rasa rayukansu wajen kare jama’a,” in ji gwamnan.

Gwamna Lawal ya kuma shawarci mambobin majalisar da su ci gaba da kyakkyawar dangantaka da sauran jami’an gwamnati da zababbun wakilai domin tabbatar da ingantacciyar gwamnati da samar da ayyuka ga jama’a.

 

AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tsaro Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ɗauki matakin rage shan gishiri a Nijeriya

Gwamnatin Tarayya ta ƙudiri aniyar rage kaso 30 cikin 100 na sinadarin gishiri (sodium) a kowane nau’in abincin ɗan fakiti da ake sayarwa a kantuna da wuraren kasuwanci a kasar.

Aminiya ta ruwaito cewa gwamnatin za ta soma aiwatar da wannan shirin ne a bana domin daƙile cutar hawan jini da dangoginta a ƙasar.

Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano An kama sojoji 20 kan yunƙurin kifar da gwamnatin Tinubu

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin lafiya kuma jakadiyar manufofin rage gishiri, Dokta Salma Ibrahim Anas, ce ta bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar a fadar shugaban kasa yayin bikin Ranar Abinci ta Duniya ta 2025 a Abuja.

A cewarta, wannan matakin na tafiya ne da ƙa’idar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), kuma yana cikin sauye-sauyen da ake aiwatarwa a fannin lafiya ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata (Renewed Hope Agenda) na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

“Gwamnatin Tarayya ta hannun Ma’aikatar Lafiya da Walwalar Jama’a tare da Hukumar NAFDAC ta kammala shirye-shiryen ƙirƙirar dokar rage gishiri a abinci.”

“Sannan kuma akwai dokar da za ta tilasta bayyana duk sinadarai da adadinsu a jikin kowane abinci ɗan fakiti (Front-of-Pack Labelling Framework) domin taimaka wa ‘yan Najeriya wajen yin zaɓin abinci mai lafiya,” in ji ta.

Ta bayyana cewa shan gishiri fiye da kima na daga cikin manyan abubuwan da ke jawo hawan jini, da sauran cututtuka masu nasaba da zuciya a ƙasar.

Dokta Salma ta bayyana cewa sama da kashi 35 cikin 100 na wadanda suka manyanta a Najeriya na fama da hawan jini saboda yawan shan gishiri fiye da ƙa’idar WHO wato gram biyar a rana.

“Rage yawan shan gishiri zai taimaka wajen inganta lafiyar jama’a da rage kuɗin da ake kashewa wajen jinyar cututtukan da za a iya kauce musu,” in ji ta.

Shugaban cibiyar Network for Health Equity and Development (NHED), Dokta Jerome Mafeni, ya ce dokar rage gishiri da tsarin lakabin bayanai na jikin abinci muhimman matakai ne da za su taimaka wajen hana yaduwar cututtuka masu tsanani.

“Wadannan manufofi biyu suna aiki tare — ɗaya yana kayyade yawan gishiri a abinci, ɗayan kuma yana taimaka wa masu amfani da abinci su gane bayanai cikin sauƙi domin su yi zabi mafi kyau,” in ji shi.

Dr. Mafeni ya ce irin waɗannan manufofi a wasu ƙasashe sun taimaka wajen rage yawan shan gishiri da ƙara wayar da kan jama’a kan lafiyayyen abinci.

Ya ƙara da cewa rashin cin abinci mai kyau na rage ƙarfin aiki da ƙara kashe kuɗin jinya a gidaje, don haka rage gishiri ya zama al’amari na ci gaban ƙasa.

Wakiliyar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), Dr. Mya Sapal Ngon, ta ce suna goyon bayan shirin rage ta’ammali da gishiri a Najeriya, tare da tabbatar da ci gaba da taimakawa wajen aiwatar da manufofi da ke inganta lafiyayyen tsarin abinci.

“WHO za ta ci gaba da tallafawa Najeriya wajen aiwatar da dokokin da za su taimaka wajen kare lafiyar jama’a,” in ji ta.

“Haka kuma, kafafen yada labarai na da rawar da za su taka wajen fadakar da jama’a kan illolin shan gishiri fiye da kima da amfanin samun bayanai kan sinadarai a abinci.”

Dokta Anas ta tabbatar da cewa fadar shugaban kasa za ta ci gaba da hada kai da hukumomi da kungiyoyi domin karfafa matakan kare lafiyar jama’a, “kare lafiyar ‘yan Najeriya na nufin kare makomar ƙasa,” in ji ta.

Dokta Salma Ibrahim Anas

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro
  • Sanata Barau Ya Kai Ziyarar Gani Da Ido Aikin Da Ake Yi A AKTH
  • An dawo da malamai 103 da aka kora daga aiki a Zamfara
  • Talauci ne babban maƙiyin ɗan Adam — Atiku
  • Gwamnati ta ɗauki matakin rage shan gishiri a Nijeriya
  • An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
  • Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul
  • HOTUNA: Al’ummar Jihar Neja sun yi addu’o’in neman zaman lafiya
  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro