Uba Sani ya yi wa ma’aikatan manyan makarantu ƙarin kashi 70 a albashi
Published: 21st, October 2025 GMT
Gwamnan Kaduna, Sanata Uba Sani, ya amince da aiwatar da ƙarin kashi 70 a albashin ma’aikatan dukkanin makarantun gaba da sakandare na gwamnati da ke jihar.
Sabon tsarin albashin na CONPCASS/CONTEDISS 2024 wanda zai fara aiki daga Oktoban 2025, na daga cikin kokarin gwamnatinsa na inganta walwalar ma’aikata da farfaɗo da harkar ilimi a jihar.
Amincewar na zuwa ne bayan wani muhimmin zama da aka gudanar tsakanin gwamnan da shugabannin ƙungiyoyin ma’aikatan manyan makarantu (JUTIKS), wanda hakan ya kai ga janye yajin aikin da aka shafe wata guda ana yi.
Taron wanda Ƙungiyar Ƙwadago ta NLC ta shirya kuma aka gudanar a fadar gwamnatin Kaduna, ya samu halartar shugabannin ƙungiyoyi daga Nuhu Bamalli Polytechnic da ke Zariya, da Kwalejin Ilimi ta Gidan Waya, da kuma Kwalejin Nazarin Jinya da Ungozoma ta Kaduna.
Ana iya tuna cewa, tun a ranar 30 ga watan Satumban da ya gabata ne ma’aikatan manyan makarantun suka tsunduma yajin aikin neman a aiwatar da tsarin albashi na CONPCASS/CONTEDISS na 2009, da kuma inganta fansho da walwalar ma’aikata gaba ɗaya.
A wani taron manema labarai da shugabannin ƙungiyoyin suka gudanar, sun yaba da jajircewar gwamna Uba Sani wajen kare haƙƙin ma’aikata da bai wa ilimi fifiko.
Haka kuma, sun jinjina wa gwamnatin bisa rage kuɗin makaranta da kashi 50% a dukkanin manyan makarantu, da kuma gyare-gyaren gine-gine da kayan aiki da ake ci gaba da yi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kaduna manyan makarantu
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru
Tsohon Ministan Tsaro, Abubakar Badaru, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya san dalilin da ya sa ya yi murabus.
Badaru, ya ajiye aiki ne a ranar Litinin, inda ya ce matsar rashin lafiya ce ta sa ya yi murabus.
Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokintaShugaban ƙasa ya amince da murabus ɗinsa kuma ya naɗa Janar Chris Musa a matsayin sabon Ministan Tsaro.
Badaru, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa ya yi murabus ne saboda barazanar da Amurka ta yi na ɗaukar matakin soji kan Najeriya game da zargin kisan Kiristoci.
“Ina so na bayyana a fili cewa wannan labari ƙarya ne, an ƙirƙire shi don ɓata min suna, kuma ba shi da alaƙa da ni ko wani da ke magana a madadina,” in ji shi.
Ya ce an ƙirƙiro wannan ƙarya ne don a ɓata masa suna da kuma haddasa rikici tsakaninsa da shugaban ƙasa.
“Gaskiyar dalilin murabus ɗina na bayyana ta shugaban ƙasa. Duk wani ƙarin bayani na daban ƙarya ne da aka ƙirƙira,” in ji Badaru.
Ya tabbatar wa Tinubu da ’yan Najeriya cewa har yanzu yana biyayya, tare da jajircewa wajen ganin an samu zaman lafiya, tsaro da nasarar jam’iyyar APC kafin zaɓen 2027.