Jihohin Jigawa, Katsina da Kano sun amince da hadin gwiwa kan kasuwar wutar lantarki ta jihohi uku, tare da samun kaso a kamfanin Future Energies Africa (FEA), wanda shi ne ke da hannun  jari mafi girma a Kano Electricity Distribution Company (KEDCO).

Kwamishinan wutar lantarki na jihar Jigawa, Injiniya Surajo Musa, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Dutse.

Ya ce gwamnonin jihohin ukun sun cimma wannan matsaya ce a birnin Marrakech, kasar Morocco, yayin taron kolin manyan jami’ai kan samar da wutar lantarki.

Injiniya Surajo Musa ya kara da cewa a yayin taron, jihohin Kano da Katsina sun amince da yin hadin gwiwa da jihar Jigawa wajen samun kaso a Future Energies Africa, domin karfafa tsare-tsaren ci gaban KEDCO.

“Jihohin uku tare da kamfanin Future Energies Africa za su kaddamar da wani asusun samar da wutar lantarki na musamman  wanda shi ne irinsa na farko  da ake sa ran zai kai Naira Biliyan 50 a matakin farko, domin hanzarta samar da wuta a cikin jihohin uku,” in ji shi.

Sanarwar ta kara da cewa jihohin za su duba hanyoyin da Dokar Wutar Lantarki (Electricity Act) ta tanada, domin yin hadin gwiwa kan kasuwar wutar lantarki ta jihohin uku, inda kowanne zai amfana.

Ya ce FEA tare da gwamnonin jihohin uku za su rika gudanar da taron kasa da kasa sau daya a shekara, sannan su rika ganawa duk bayan watanni uku domin duba ci gaba da karfafa dangantakar kasuwar wutar lantarki ta Arewa maso Yamma.

 

Usman Mohammed Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale

Hassan Fadlallah wanda dan majalisar kasar Lebanon ne daga kungiyar Hizbullahy a bayyana cewa; gwargwadon yadda ake ja da baya a gaban makiya, suke kara samun karfin gwiwa,don haka da akwai bukatar hadin kai a tsakanin kasashen larabawa da na musulmi domin fuskantar kalubalen dake gaba.

 Shi dai Hassan Fadlalalah yana halartar taron majalisun kasashe  nahiyar Asiya da ake yi a birnin Mashhad na Iran, ya bayyana cewa: Laifukan da ‘yan sahayoniya suke yi, yana nuni ne da yadda su ka kai koli wajen nuna keta a kan kasashen da suke da cin gashin kai da ‘yanci, da hakan yake a matsayin karya zaman lafiya da sulhu na duniya.

Fadlallah ya kuma yi jinjina ga jamhuriyar musulunci ta Iran akan tsayin dakarta a lokacin wuce gona da irin Haramtacciyar Kasar Iran da kuma kare kanta da ta yi wanda halartacce ne kamar yadda dokokin kasa da kasa su ka yi tanadi.

Haka nan kuma ya ci gaba da cewa; Haramtacciyar kasar Isra’ila ta kuma kai wasu hare-haren wuce akan kasashen Yemen da Qatar,wanda abin yin Allawadai da shi ne.

Dan majalisar kasar ta Lebanon ya kuma yi Ishara da yadda sojojin mamayar Haramtaccitar kasar Isra’ila suke kai wa kasar Syria hare-hare daga lokaci zuwa lokaci domin damfara ikonta a kan wannan kasa.

Bugu da kari, Hassan Fadlallah ya yi kira da dukkanin al’ummun larabawa da na musulmi da su  yi watsi da sabanin dake tsakaninsu domin fuskantar kalubalen da yake a tsakaninsu.

A gefe daya, dan majalisar na Iran ya gana da shugaban Majalisar shawarar musulunci ta Iran Muhammad Bakir Qalibaf, tare da mi ka masa gaisuwa daga shugaban majalisar dokokin kasar Lebanon Nabih Barry.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka  Jiragen Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon December 4, 2025  An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila December 4, 2025 An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya December 4, 2025 Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata December 4, 2025 Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe December 4, 2025 MDD ta nemi a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma Tuddan Golan December 4, 2025 Rundunar Ruwa ta IRGC na Gudanar Da Atisayen Soja a Tekun Fasha December 4, 2025 Dan wasan Taekwando Na kasar Iran Ya Samua Lambar Yabo Ta Zinariya December 4, 2025 Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin  Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Gaza December 4, 2025 Iran: Tsaron Yankin Tekun Fasha Jan Layi Ne Da Za’a Fuskanci Mayar Da Martani Adan Aka Taba Shi December 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha
  • Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe
  • NAJERIYA A YAU: Abun Da Masu Ruwa Da Tsaki Ke Yi Na Dakile Laifuka A Wurin Matasa
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina