Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni
Published: 21st, October 2025 GMT
“Wadanda aka nada sun bayyana a gaban kwamitin don tantancewa a ranar Talata, 14 ga Oktoba, 2025,” in ji shi. “Kwamitin bai samu koke ko korafe-korafe ba a kansu, sun nuna shiri da cancanta akan ayyukan da aka zabo su”.
Ya bayyana sunayen wadanda aka tantance a matsayin: “Aminu Yusuf (Jihar Neja) – Shugaba, Joseph Haruna Kigbu (Jihar Nasarawa) – Kwamishina, Tonga Betara Bularafa (jihar Yobe) – Kwamishina.
এছাড়াও পড়ুন:
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447
Sanarwar ta ce, “Domin rage wahalhalun da al’umma ke fuskanta wajen samun kula da lafiya, gwamnatin Dauda Lawal ta ƙaddamar da wannan shiri na musamman domin tallafa wa masu ƙaramin ƙarfi da ke buƙatar jinya.”
Shirin, wanda aka fara a watan Agusta 2023, ya riga ya isa ga marasa lafiya sama da 3,400 zuwa asibitoci daban-daban ta hanyar tsarin ‘tele-screening’, wanda ke bai wa ƙwararrun likitoci damar lura da marasa lafiya daga ƙauyuka da yankunan karkara cikin gundumomi 14 na jihar.
Bangarorin da aka kula da lafiya a zagaye na goman da suka haɗa da; mutum 1,659 marasa lafiya masu kumburin ciki da irin sa. Mutum 1,081 masu ciwon ido da aka yi wa tiyata. Mutum 118 marasa lafiya masu cutar VVF da aka yi wa tiyata.
Sanarwar ta bayyana cewa, wannan shiri ya zama wata nasara ga gwamnatin jihar wajen kai ingantacciyar kulawar lafiya ga jama’a, musamman a yankunan da ke da ƙarancin cibiyoyin jinya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA