AGILE Kano Ta Tattauna da Malamai da Limamai Don Ƙarfafa Goyon Bayan Ilimin ’Yan Mata
Published: 24th, October 2025 GMT
Shirin karfafa ilimin ‘ya’ya mata a jihar Kano ya shirya taron tattaunawa da malamai da limaman masallatan Juma’a domin ƙarfafa haɗin gwiwa da shugabannin addini wajen inganta goyon bayan al’umma ga ilimin ’yan mata a fadin jihar.
Taron, wanda yake ɗaya daga cikin dabarun haɗin kai na masu ruwa da tsaki na AGILE, yana da nufin ƙara samun damar karatu, tsayawa da kuma kammala karatun ’yan mata ta hanyar daidaita ayyukan shirin da dabi’u da imanin al’umma.
A jawabinsa, Shugaban Shirin AGILE na Jihar Kano, Malam Mujtapha Aminu, ya bayyana cewa an shirya taron ne domin fayyace wasu rashin fahimta da ake da su game da shirin, da kuma tabbatar da fahimtar juna tsakanin shugabannin addini.
A cewarsa, “Shigar malamai da limaman masallatan Juma’a cikin wannan shiri yana da matuƙar muhimmanci domin suna da tasiri wajen gina ra’ayin jama’a. Mun gayyace su ne domin mu wayar da kan su game da manufofi, sassa, da matakan aikin shirin AGILE.”
Malam Mujtapha ya ƙara bayyana cewa shirin ya riga ya haɗa kai da shugabannin gargajiya da na addini wajen duba kundin horarwa don tabbatar da cewa yana tafiya da koyarwar addinin Musulunci da kuma dabi’un Hausawa.
Ya roƙi dukkan masu ruwa da tsaki da su ci gaba da ba da goyon baya ga shirin tare da neman bayani a duk lokacin da wani abu ya taso, domin kauce wa rashin fahimta. Ya jaddada cewa, “Malamai sune manyan masu tasiri wajen bunƙasa ilimin ’yan mata a Kano da Najeriya gaba ɗaya.”
A sakon sa na fatan alheri, Shugaban Majalisar Malamai ta Jihar Kano, Sheikh Ibrahim Khalil, wanda Sakatarensa Sheikh Ibrahim Abubakar Tofa ya wakilta, ya shawarci tawagar AGILE da su tabbatar dukkan sassan shirin suna tafiya da ka’idojin Musulunci da al’adun mutanen Kano, domin jihar na da tsarin rayuwa mai zurfi da al’adu masu ƙarfi.
Ya ce, “A matsayarmu na manyan masu ruwa da tsaki, muna da muhimmiyar rawa wajen tallafa wa ilimin ’yan mata domin Musulunci yana ƙarfafa neman ilimi ga maza da mata duka.”
Haka kuma, ya yi kira ga masu gudanar da shirin da su ci gaba da haɗa kai da dukkan masu ruwa da tsaki don gujewa yaɗuwar bayanan ƙarya da kuma tabbatar da gaskiya a duk matakan aiwatarwa.
Taron ya ƙunshi gabatar da cikakkun bayanai kan manyan sassan uku na shirin AGILE, tattaunawa tsakanin mahalarta, da zaman tambayoyi da amsoshi inda malamai suka gabatar da tambayoyi kan wasu bangarorin shirin kuma aka basu bayanai dalla-dalla.
Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: masu ruwa da tsaki
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan uwana 8 sun rasu a fashewar tanka a Neja — Wani Mutum
Wani mutum mai suna Mallam Surajo Muhammad Shehu ya rasa ’yan uwansa takwas, lokacin da tankar mai ta yi bindiga a garin Essa da ke kan hanyar Agaie zuwa Bida, a Jihar Neja.
Lamarin ya auku a ranar Talata, wanda aƙalla mutum 28 ciki har da mata da ƙanana yara, suka rasa rayukansu lokacin da tankar ta kife kuma ta kama da wuta yayin da jama’a ke ƙoƙarin ɗibar mai.
Tun da PDP ta bar mulkin Najeriya maguɗin zaɓe ya ragu – Akpabio Dangote zai sayar da kaso 10 na hannun jarin matatar man shiWasu da dama sun ji rauni kuma an garzaya da su Asibitin Gwamnatin Tarayya (FMC) da ke Bida.
Shehu, ya ce mata ne suka fi mtuuwa saboda maza sun tafi gona lokacin da lamarin ya faru.
Ya zargi mazauna yankin da ƙin bin gargaɗin da aka sha yi musu kan hatsarin ɗibar mai daga tankar da ta kife.
Hakimin Essa, Alhaji Adamu Bagudu, ya tabbatar da cewa an binne mutum 28, ciki har da mata 24.
Ya ce an sha gargaɗin jama’a kan hatsarin wannan ɗabi’a, amma talauci da wahalar rayuwa ya sa mutane yin watsi da igargaɗin
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), ta ce aƙalla mutum 80 lamarin ya shafa, inda aka kai wasu 17 Abuja domin samun kulawa ta musamman.
Gwamnan Gombe kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Inuwa Yahaya, ya bayyana alhininsa kan lamarin tare da kiran gwamnati da ta ƙara tsaurara matakan tsaro da kuma gyaran hanyoyi.
Majalisar Wakilai ta Ƙasa ta kuma roƙi Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta gyara hanyar Bida zuwa Agaie wadda ke janyo salwantar rayukan mutane.