Aminiya:
2025-10-24@20:35:14 GMT

‘Yan sanda sun kama ɗalibi da ya soki Gwamnan Neja

Published: 24th, October 2025 GMT

Rundunar ’yan sanda ta kama wani matashi ɗan shekara 29, mai suna Abubakar Isah Mokwa ɗalibi da yake karatun digiri na biyu a tsangayar Tattalin Arziki na Noma a Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai, Jihar Neja.

An kama ɗalibin ne bisa zarginsa da sukar Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago.

Rahotanni sun ce an an kama Abubakar Mokwa ne a wajen harabar jami’ar da yake da masauki a Lapai a ranar Alhamis bayan wani saƙon da ya wallafa a shafinsa na Facebook inda ya caccaki gwamnan kan rashin aikin yi.

’Yan sanda sun sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa Tinubu ya sauke hafsoshin tsaro, ya maye gurbinsu da wasu

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun ne ya tabbatar wa Aminiya kamun da aka yi wa ɗalibin.

Ya ce, an kama wanda ake zargin ne biyo bayan ƙorafin da ya yi kan cin zarafi ta intanet, satar bayanai ta intanet da sauran laifukan da suka shafi intanet.

“Rundunar ’yan sandan Jihar Neja ta samu ƙorafin aikata laifukan da suka haɗa da cin zarafi ta intanet, satar bayanai ta intanet da sauran laifukan da suka shafi intanet akan wani Abubakar Isah Mokwa mai shekara 29 a garin Mokwa kuma ɗalibin IBBUL da yake karatun digiri na biyu.

“Saboda haka, hukumar jami’an Lapai ta gayyace shi ta kama shi a ranar 23 ga Oktoba, 2025 da misalin ƙarfe 11 na dare, sannan aka tura shi hedikwatar ‘yan sanda ta jihar a Minna babban birnin jihar, domin ci gaba da bincike kan ƙarar da ake tuhumarsa da aikatawa. Sai dai wanda ake zargin yana tsare kuma za a ci gaba da yi wa jama’a ƙarin bayanui,” in ji Abiodun.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Ibrahim Badamasi Babangida Jihar Neja

এছাড়াও পড়ুন:

Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

A shekara biyu kaɗai,ya yi ƙoƙarin maida Jihar Kaduna da aka sani da rarrabuwar kai, yanzu ta koma tsintsiya ɗaya sanadiyar hakan.

Yin gyara ta hanyar ci gaba

Gwamna Sani ya hau kan karagar mulki ne a shekarar 2023 ba a matsayin wanda ya iya lamarin siyasa sosai ba, sai dai mai son kawo agyara. Aikinsa na farko ba siyasar bace —mutane ne yafi maida hankali kansu.

Ya fara ƙaddamar da lamarin gaggarumin ci gaban ƙauyuka ta yadda abin ya zama a kowace ƙaramar hukumar akwai aikin da ake yi.Gina hanyoyi, asibitoci,  makarantu, kasuwanni an fara gigginasu a ƙananan hukumomi  23 .

Cikin ci gaban daya samu sun haɗa da:

Haɓaka ƙananan asibitoci 225 inda aka mayar da su matsayi na 2, inda tuni aka kammala 174.

An gyara 13 daga cikin manyan asibitoci 33 da kuma sa masu dukkan kayan da suka kamata.

Gadaje 300- na asibitin ƙwararu, da aka yi watsi da shi tun shekarar 2009, an kammala su, Shugaban ƙasa Bola Tinubu — ya ƙaddamar dasu inda aka kawo ƙarshen shekara 16- da aka yi ana jira.

Manyan motoci 400 da suke ɗauke da Takin zamanin da aka rabawa ƙananan manoma 100,000 kyauta, domin samun ingantaccen abinci maikyau da kuma isasshe.

Kowane aikin da aka yi akwai labarain da yake badawa na dalilin da yasa aka yi shi — na gwamnan da shi manufarsa ita ce kowanne al’umma a Jihar Kaduna.,ko  a Birni suke ko kuma ƙauye, su san da cewa ba mantawa aka yi dasu ba.

Abubuwan more rayuwa ta hanyar sasantawa

Babban burin shi mai sauƙi ne babu wata wahala: ci gaba shi ne babban lamarin tafiya da haɗin kai domin sasantawa.

Yadda aka yi ayyukan a dukkan faɗin Jihar ba tare da la’akari da Kabila ba ko kuma addini, ballantana ma har ace daga wace shiyya mutum yake, ya koyar da amincewa da yarda a cikin Jihar duk kuwa yadda take da al’umma daban- daban.

A ƙoƙarinsa na haɓaka hanyoyi, kilomitoci na manyan hanyoyi yanzu an haɗa su, waɗanda a shekarun baya an raba mutane da zuwa kasuwannin ƙauyuka. Gadoji waɗanda suka haɗa  garuruwa— yanzu sun koma wata dabarar sake haɗa al’ummar da a da basu ga maciji koi zaman manja da doya tsakaninsu, domin da a rabe suke sanadiyar rashin jituwa.

Kaduna a halin da ake ciki yanzu babu wata maganar rarrabuwar kai sai dai ƙarin danƙon- zumunci.

Mai son bunƙasar Mata da Matasa

Gwamna Sani bai tsaya anan ba domin kuwa suma Mata da matasa abin ci gaban ya same su domin kuwa ba mantawa ya yi dasu ba.

A hanyar gidauniyar Uba Sani, an horar da dubban matasa wajen koyon sana’oi, koyon yadda za’a tafiyar da na’urar sadarwa ta zamani, da kuma dabarun sana’oi daban- daban. An kuma raba masu tallafin yadda za su fara sana’oi da wasu kayayyaki waɗanda zasu ɗaukaka mata daga dogaro da wasu, su zama masu nema ba dai a nemo a basu ba.

Hakanan ma ya buɗe hanya inda har ila yau ya taimakawa mata da matasa waɗanda aka sa su wasu wurare masu amfani, inda yake nuna cewa yadda Jihar zata kasance, a gaba abin ya dogara ne kan dukkan al’ummarta gaba ɗaya.

Ya san yadda zai yi mu’amala da mutane

Kafin ya shiga gidan gwamna, Uba Sani ya fara rayuwar zuwa gidan gwamnati ne da zama da zama ɗan gwagwarmaya, ɗan kasuwa, da kuma ma’aikaci —lamarin da kowa yake haɗa hakan ba, shi yasa kuma yadda yake tafiyar da gwamnatinsa abu ne mai sauƙi gare shi.

Ƙuniya mai zaman kanta : A matsayin mataimakin  shugaban na ( Arewa) fafutukar kamfen na damukuraɗiyya, daga baya kuma mataimakin Shugaba  (Arewa)  na JACON ada ke ƙarƙashin Chief Gani Fawehinmi, a  Arewacin Nijeriya zamanin mulkin soja.

Kasuwanci: Ɗan kasuwa ne wanda ya samu nasara a harkar  sadarwa  da kuma gidaje da filaye, daga can ne ya koyi haƙuri idan ya samu riba ko kuma faɗuwa.

Gwamnati: Matsayin Sanata (2019-2023) , yayi shugbancin kwamitin Banki, Inshora da sauran hukumomi masu harkar kuɗaɗe ya bada gudunmawa wajen gyaran da aka yi wanda shi ne ya ƙara haɓaka lamarin kuɗaɗe.

Irin halayya ta gwagwarmaya, kasuwanci, da kum atsarin manufofi hakan ya samar da Shugaba kuma jagora, wanda idan aka aikata rashin adalci zai nuna rashin adalci, akwai ranar da zai nemi ayi zaman sulhu.

Mai ra’ayin ilimi, yin abu yadda ya dace ayi shi, da kuma mutuntawa

An haife shi ranar 31 ga Disamba 1970, a Zariya, Sani yana digiri na biyu a harkokin da suka shafi kuɗi daga Jami’ar Kalaba, sai Difiloma kan harkokin mulki daga Jami’ar Abuja , da kuma Babbar Difiloma ta ƙasa kan  Makanikal Injiniya daga makarantar  fasaha ta Kaduna.

Hakanan ma shi shi tsohon ɗalibi ne na  wani karatun da yayi kan Shugabanci  a Amerika. (IƁLP) “yin abu ba tare da amsar ko kwabo ba, sai yadda za ‘a tafiyar da ƙungiyoyi masu zaman kansu.”

Karatuntukan makarantun da yayi ko shakka babu sun kasance fitila gun shin a yadda zai tafiyar da harkokin gwamnati da dai sauran al’amura.

Daga majalisa zuwa gidan gwamnati

A matsayin san a Sanata, Uba Sani ya bar wani abinda ya zama tarihi. Uku daga cikin ƙudurorinsa sun samu amincear Shugaban ƙasa — lamarin da ba kowa bane zai samu irin wannan sa’ar — hakan ne ma yasa ake girmama shi a matsayin ɗan majalisa da yafi amfani a majalisar ƙasa ta 9.

Sa’oin daya samu sun nuna cewar horon ya yi matuƙar taimaka ma shi wajen yadda yake tafiyar da mulkin Jihar Kaduna.

Yanzu shi ne, mataimakin ƙungiyar gwamnonin APC shi ne kuma gwamna da zai sa ido kan lamauran sashen Arew a maso yamma, da kuma daidaituwar manufofin gwamnatin tarayya da Jihohi.

Shugaba mai sauraren jama’arsa

A Jihar Kaduna, koda waɗanda basu yin shi sun amince da gwamna Uba Sani ya na tafiyar da mulkinsa kamar yadda ya dace.

Yana ganawa da al’umma kafin motar da zata yi gyara ta kama aikinta, zai saurare su kafin ya ɗauki mataki, a wurin shi kuma dole ne tilastawa ta biyo bayan tausayawa.Yadda yake sauraren al’umma yasa suna amincewa da duk waɗansu abubuwan daya kawo gabansu tsakanin Sarakunan gargajiya, Shugabannin addini, da kuma ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Ba wani abin mamaki bane tunda yanzu tarurrukan zaman lafiya yanzu sun fi zanga- zanga, ga kuma uwa- uba yadda ake haɗa kai tsakanin al’ummomi shi ne ya maye gurbin yadda ake zama a shekarun baya.

Ayyukan da ya yi sun sa amincewa da yadda yake

Gwamnan Kaduna Uba Sani ba wai ya fi kowa iya mulki bane, amma akwai ci gaba a Jihar saboda da akwai yarda juna, wanda ta hakan ma ana samun ci gaba.

Mulkinsa ya maida hankali ne kan abubuwan more rayuwa, kula da lafiyar al’umma, aikin moma, da kuma masana’antu, irin hakan ne ya jawo hankalin al’umma a iyakokin Nijeriya.

Shi ya sa mutane ke son tun daga zucci, ɗan gwagwarmayar da ya taɓa yi zanga- zanga domin a wanzar da mulkin farar hula —yanzu shi ne mai gina damukuraɗiyya da hanyoyi, makarantu, da kuma asibitoci.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma October 24, 2025 Manyan Labarai An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya October 24, 2025 Manyan Labarai Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu October 24, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun sake kama Sowore bayan kotu ta bayar da belinsa
  • Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu
  • An kama Sakataren APC na mazaba a Yobe kan zargin aikata kisan kai
  • Gwamnan Neja ya ba dukkan iyalan wadanda suka kone a gobarar tankar mai N1m
  • Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna
  • Gwamnatin Tarayya ta yi jimami kan mutuwar mutanen da suka rasu a fashewar motar mai a Jihar Neja
  • Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar mutanen da suka rasu a fashewar tanka a Neja
  • Rundunar ‘Yan Sanda A Jihar Zamfara Ta Gargadi Direbobi Game Da Rufe Lambar Mota
  • Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja