Aminiya:
2025-10-21@20:02:05 GMT

Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsa

Published: 21st, October 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya sanar da shirinsa na ɗaga darajar Kwalejin Jinya ta Nafisatu da ke Kwankwaso zuwa cikakkiyar Jami’ar Kiwon Lafiya albarkacin bikin zagayowar ranar haihuwarsa.

Taron na wannan Talatar, 21 ga watan Oktoban 2025, ya gudana ne a garinsa na Kwankwaso da ke Karamar Hukumar Madobi, inda aka yaba da ci gaban da makarantar ta samu tun daga kafuwarta a 2019 zuwa yanzu.

Tinubu ya naɗa sabon Minista Alƙaluman wucin-gadi na nuna Paul Biya ya lashe zaɓen Kamaru

Kwankwaso ya ce an ɗauki wannan mataki ne domin ƙara buɗe damammaki ga mata matasa su sami ilimin kiwon lafiya mai zurfi.

Ya jaddada cewa makarantar ita ce ta farko a Najeriya da ke karɓar dalibai mata kaɗai.

Ya kuma gode wa gwamnatin Jihar Kano bisa tallafa wa shirin ungozoma na Community Midwives, wanda ke taimakawa wajen inganta lafiyar mata a ƙauyuka.

A nasa jawabin, Farfaesa Saleh Ngaski Garba, shugaban majalisar gudanarwar makarantar, ya bayyana cewa kwalejin ta taimaka sosai wajen bai wa mazauna ƙauyen ilimin jinya da ungozoma, kuma yanzu tana da ɗalibai sama da 400 da suka kammala karatu.

Kwankwaso ya ce gina jami’ar zai amfanar da Kano da Najeriya baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Kiwon Lafiya Kwalejin Lafiya ta Nafisatu Kwankwaso Sanata Rabi u Musa Kwankwaso Kwankwaso ya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tun bayan fara shari’ar Nnamdi Kanu a shekarar 2021 mutane da dama suke bayyana ra’ayoyinsu a kan sake shi ko a kyale shari’a ta yi halinta.

 

Hasali ma har zanga-zanga wasu ‘yan Najeriya suka kira don bayyana bukatar sakin shugaban na ‘yan aware.

NAJERIYA A YAU: Yadda Cire Darasin Lissafi Zai Taimakawa Dalibai Shiga Jami’a DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan ko ya dace a saki Nnamdi Kanu?

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Muka Shiga Sakamakon Haihuwar ’Ya Mai Cutar Motsewar Kwakwalwa
  • Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu
  • APC ta rage wa Mata kuɗin tsayawa takara a Borno
  • Yadda Morocco ta kafa tarihin ɗaga Kofin Duniya na FIFA U20
  • Kano Pillars ta dakatar da Kocinta
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?
  • Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?
  • An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
  • An kama sojoji 20 kan yunƙurin kifar da gwamnatin Tinubu