Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsa
Published: 21st, October 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya sanar da shirinsa na ɗaga darajar Kwalejin Jinya ta Nafisatu da ke Kwankwaso zuwa cikakkiyar Jami’ar Kiwon Lafiya albarkacin bikin zagayowar ranar haihuwarsa.
Taron na wannan Talatar, 21 ga watan Oktoban 2025, ya gudana ne a garinsa na Kwankwaso da ke Karamar Hukumar Madobi, inda aka yaba da ci gaban da makarantar ta samu tun daga kafuwarta a 2019 zuwa yanzu.
Kwankwaso ya ce an ɗauki wannan mataki ne domin ƙara buɗe damammaki ga mata matasa su sami ilimin kiwon lafiya mai zurfi.
Ya jaddada cewa makarantar ita ce ta farko a Najeriya da ke karɓar dalibai mata kaɗai.
Ya kuma gode wa gwamnatin Jihar Kano bisa tallafa wa shirin ungozoma na Community Midwives, wanda ke taimakawa wajen inganta lafiyar mata a ƙauyuka.
A nasa jawabin, Farfaesa Saleh Ngaski Garba, shugaban majalisar gudanarwar makarantar, ya bayyana cewa kwalejin ta taimaka sosai wajen bai wa mazauna ƙauyen ilimin jinya da ungozoma, kuma yanzu tana da ɗalibai sama da 400 da suka kammala karatu.
Kwankwaso ya ce gina jami’ar zai amfanar da Kano da Najeriya baki ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jami ar Kiwon Lafiya Kwalejin Lafiya ta Nafisatu Kwankwaso Sanata Rabi u Musa Kwankwaso Kwankwaso ya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya ce ba zai bai wa ’yan Najeriya kunya ba, saboda ƙwarin guiwar da suke da shi a kansa.
Musa, wanda Shugaba Bola Tinubu ya naɗa ministan tsaro, ya bayyana haka ne a ranar Laraba lokacin da aka tantance shi a Majalisar Dattawa.
Tsaro: Gwamnonin Arewa na shirin dakatar da haƙar ma’adinai Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyuYa gode wa Shugaban Ƙasa saboda zaɓarsa da ya yi a matsayin minista, sannan ya gode wa ’yan Najeriya saboda amincewa da suka yi da shi.
Ya yi alƙawarin yin iya bakin ƙoƙarinsa domin tabbatar da zaman lafiya a ƙasar nan.
Ya ce: “Da na ga irin martanin mutane bayan an ambaci sunana, na san cewa ba zan bari na gaza ba, ba zan bai wa ’yan ƙasata kunya ba. Duk abin da ya kamata mu yi, za mu yi, kuma na san da taimakon Allah za mu yi nasara.”
Musa ya ƙara da cewa abin ya ba shi mamaki ganin irin goyon bayan da aka ba shi a kafafen sada zumunta.
“Na je kafafen sada zumunta kuma abin ya ba ni mamaki ganin irin martanin mutane. Wannan yana nuna cewa mutane suna son ganin Najeriya ta zauna lafiya.”
Ya ce wasu suna cewa ’yan Najeriya ba sa son Najeriya, amma bai yadda da wannan batu ba.
“Idan wasu suna cewa ’yan Najeriya ba sa son ƙasarsu ina cewa ba haka abun yake ba, ba su san ’yan Najeriya ba.”
Ya kuma yi magana kan kashe-kashen da ake fama da su a wasu sassan ƙasar nan.
“Ko a kira shi kisan ƙare-dangi ko akasin haka, matsalar na shafarmu baki ɗaya. Ana kashe mutane ko ina,” in ji shi.
Ya jaddada cewa dole ne a haɗa kai don shawo kan matsalar.
“Shi ya sa ya zama dole mu yi aiki tare. Idan muka bar giɓi, su ne za su samu wajen shiga. Ba sa damuwa da wanda za su kashe. Waɗannan mutane mugaye ne, da yawa daga cikinsu ma suna shan miyagun ƙwayoyi.
“Saboda haka dole a kawo ƙarshen kashe-kashen nan. Manufarmu ita ce mu fuskance su kai-tsaye mu kuma dakatar da waɗannan kashe-kashen.”