Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da aikin gina hanyar Babban Sara zuwa Malam Bako zuwa Shabaru zuwa Kirgi zuwa Albasu, mai tsawon kilomita 28.2, a Karamar Hukumar Sule Tankarkar,wanda kudinsa ya kakaNaira Biliyan 4.47, a ci gaba da shirin Gwamnati da Jama’a.

Aikin hanyar zai hada fiye da kauyuka 60 tare da karfafa harkokin kasuwanci da zamantakewa a yankin.

Haka kuma, gwamnan ya bude sabuwar cibiyar kula da lafiya ta farko, da makarantar Tsangaya ta zamani, da kuma rukunin samar da ruwa a yankin.

Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin Gwamnati da Jama’a hanya ce ta karfafa gaskiya, bayyana ayyuka da kuma baiwa jama’a damar fadin  ra’ayoyinsu.

“Mun zo ne mu nuna abin da muka cimma cikin shekara biyu, mu kuma saurari jama’a domin mu kara gyara inda ya kamata,” in ji shi, yana mai jaddada cewa hakikanin gwamnati ita ce wadda ke bautar al’umma.

Ya gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa gyare-gyaren da ke karfafa tattalin arzikin jihohi da kananan hukumomi, inda ya bayyana cewa Jihar Jigawa na daga cikin jihohi shida da aka zaba don fara shirin ciyar da dalibai na National Home-Grown School Feeding Programme da aka farfado da shi.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya yaba da shirin, yana mai cewa ya zama abin koyi ga sauran jihohi wajen aiwatar da mulki tare da jama’a.

A nata jawabin, Minista a ma’aikatar  Ilimi, Farfesa Suwaiba Said Ahmad, ta jinjinawa Gwamna Namadi bisa manyan ayyukan cigaba da ke canza rayuwar jama’a.

 

Usman Mohammed Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Aikin Hanya Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja October 20, 2025 Labarai Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba October 20, 2025 Manyan Labarai ‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta October 20, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC ta ƙwato fiye da naira biliyan 500 a shekara biyu — Shetima
  • NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU
  • Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
  • Sanata Barau Ya Kai Ziyarar Gani Da Ido Aikin Da Ake Yi A AKTH
  • Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 
  • An dawo da malamai 103 da aka kora daga aiki a Zamfara
  • Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20
  • Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Bayyana Cewa: Kuduri Mai Lamba 2231 Ya Zo Karshe