Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
Published: 24th, October 2025 GMT
Gwamna Raɗɗa ya ƙara da cewa wannan zaman sulhu da ɓarayin daji da ake yi al’umma ce take yi ba wai gwamnati ba, ita gwamnati tana iya yin sulhu da ɗan bindigar da ya tuba ya yarda da zaman lafiya kuma ya ajiye mukaminsa.
A cewarsa, rawar da gwamnati take iya takawa shi ne, ta ƙarfafa zaman lafiya, sannan ta tabbatar an bi doka da oda a cikin al’umma.
Tunda farko a jawabinsa, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Hon. Nasiru Mu’azu Danmusa ya bayyana cewa Gwamna Raɗɗa ya rage ƙarfin harkokin rashin tsaro a Jihar Katsina.
Haka kuma ya bayyana cewa wannan ne karo na uku da aka ƙaddamar da bikin yaye dakarun tsaro na Malam Dikko Raɗɗa, sannan za a sake ƙaddamar da sauran a watan Nuwambar wannan shekarar idan Allah ya kai mu rai da lafiya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya
Gwamnatin kasar Rwanda ta rattaba hannu a kan yarjeniya na dalar Amurka miliyon $228 a karkashin sabon tsarin taimako na gwamnatin kasar Amurka.
Shafin yanar gizo na labarai Africa News ya bayyana cewa tallafin zai taimakawa kasar Rwanda ta kyautata harkokin kiwon lafiya a kasar ta Rwanda a yayinda tallafin kudaden zai ci gaba a sabon tsarin da gwamnatin Amurka ta fitar don tallafawa kasashen kawayenta.
Tun ran Jumma’a ne aka bada labarin kulla wannan yarjeniyar, bayanda shugaba Paul Kagame na kasar Rwanda ya rattaba hannu kan wata yarjeniya ta zaman lafiya tsakaninsa da shugaban kasar Kongo Felix tsetsekedi don kawo karshen yaki a gabacin kasar Kongo wanda kasar ta Amurka ta jagoranta.
Karkashin wannan yarjeniyar dai Amurka zata kashe dalar Amurka miliyon $158 kan kyautata kiwon lafiya a kasar Rwanda ta hanyar yakar cututtuka masu yaduwa wadanda suka hada da HIV da Malaria. Da kuma kyautata tsarin shirin ko ta kwana na bullar cututtuka masu hatsari.
Sannan Kigali zata kara dalar Amurka miliyon $70 a cikin harkokin kiwon lafiya a kasar don bayyana kekyawar anniyarta a cikin shirin kyautata kiwon lafiya a kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri December 7, 2025 Iran Ta Zama Zakaran Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21 December 7, 2025 Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi December 7, 2025 Dubban Mutane Suna Guduwa Daga Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada December 7, 2025 Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurumin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi December 6, 2025 Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci