Aminiya:
2025-12-05@07:40:18 GMT

EFCC ta ƙwato fiye da naira biliyan 500 a shekara biyu — Shetima

Published: 21st, October 2025 GMT

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arziki ta’annati ta samu nasarar tara dukiyar da ta haura naira biliyan 500 a tsawon shekaru biyu na gwamnatinsu.

Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu, ya bayyana haka ne a yayin wani taron bita da ƙara wa juna sani na alƙalai da Hukumar EFCC tare da haɗin gwiwar Hukumar Shari’a ta Najeriya (NJC) suka shirya a birnin Abuja.

Red Cross ta kafa cibiyoyin rage haɗurran bala’o’i a makarantun Gombe NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU

Shettima ya buƙaci alƙalai da sauran ma’aikatan ɓangaren shari’a da su ƙara ƙaimi tare da yin aiki bisa gaskiya da adalci, yana mai gargaɗin cewa ana fara samun matsala ne a ƙasa da zarar masu riƙe da amanar hukunci suka fara tauye haƙƙin mai haƙƙi.

Mataimakin shugaban ƙasar ya ce gwamnatinsu ba ta tsoma baki a harkokin shari’a, yana mai cewa “mun ba ɓangaren shari’a da hukumomin yaƙi da cin hanci damar gudanar da ayyukansu ba tare da katsalandan ba,” in ji shi.

Da yake bayyana irin nasarorin da aka samu a fannin yaƙi da cin hanci da rashawa, Shettima ya ce EFCC ta samu nasarar ƙwato fiye da naira biliyan 500 a cikin shekara biyu da suka gabata.

“A cikin shekara biyu na wannan gwamnatin, EFCC ta samu nasarar gurfanar da sama da mutum 7,000 a gaban kotu, sannan ta ƙwato dukiyar da ta haura naira biliyan 500,” in ji Shettima.

Ya ƙara da cewa, kuɗaɗen da aka ƙwato ana amfani da su ne a shirye-shiryen tabbatar da walwalar al’umma, ciki har da shirin bayar da bashi ga ɗalibai da sauran manufofin tallafa wa jama’a.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: naira biliyan 500

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro

Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya ce ba zai bai wa ’yan Najeriya kunya ba, saboda ƙwarin guiwar da suke da shi a kansa.

Musa, wanda Shugaba Bola Tinubu ya naɗa ministan tsaro, ya bayyana haka ne a ranar Laraba lokacin da aka tantance shi a Majalisar Dattawa.

Tsaro: Gwamnonin Arewa na shirin dakatar da haƙar ma’adinai Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu

Ya gode wa Shugaban Ƙasa saboda zaɓarsa da ya yi a matsayin minista, sannan ya gode wa ’yan Najeriya saboda amincewa da suka yi da shi.

Ya yi alƙawarin yin iya bakin ƙoƙarinsa domin tabbatar da zaman lafiya a ƙasar nan.

Ya ce: “Da na ga irin martanin mutane bayan an ambaci sunana, na san cewa ba zan bari na gaza ba, ba zan bai wa ’yan ƙasata kunya ba. Duk abin da ya kamata mu yi, za mu yi, kuma na san da taimakon Allah za mu yi nasara.”

Musa ya ƙara da cewa abin ya ba shi mamaki ganin irin goyon bayan da aka ba shi a kafafen sada zumunta.

“Na je kafafen sada zumunta kuma abin ya ba ni mamaki ganin irin martanin mutane. Wannan yana nuna cewa mutane suna son ganin Najeriya ta zauna lafiya.”

Ya ce wasu suna cewa ’yan Najeriya ba sa son Najeriya, amma bai yadda da wannan batu ba.

“Idan wasu suna cewa ’yan Najeriya ba sa son ƙasarsu ina cewa ba haka abun yake ba, ba su san ’yan Najeriya ba.”

Ya kuma yi magana kan kashe-kashen da ake fama da su a wasu sassan ƙasar nan.

“Ko a kira shi kisan ƙare-dangi ko akasin haka, matsalar na shafarmu baki ɗaya. Ana kashe mutane ko ina,” in ji shi.

Ya jaddada cewa dole ne a haɗa kai don shawo kan matsalar.

“Shi ya sa ya zama dole mu yi aiki tare. Idan muka bar giɓi, su ne za su samu wajen shiga. Ba sa damuwa da wanda za su kashe. Waɗannan mutane mugaye ne, da yawa daga cikinsu ma suna shan miyagun ƙwayoyi.

“Saboda haka dole a kawo ƙarshen kashe-kashen nan. Manufarmu ita ce mu fuskance su kai-tsaye mu kuma dakatar da waɗannan kashe-kashen.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15
  • Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
  • Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin  Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Yankin Gaza
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • Har yanzu ban bar yin waqa ba-Yusuf Lazio
  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe