An Yi Fashi Da Makami A Gidan Adana Kayan Tarihin ” Louvre” Na Kasar Faransa
Published: 21st, October 2025 GMT
Da misalin karfe 9;30 na safiyar ranar Lahadi ne dai wasu mutane masu dauke da makamai su ka kutsa cikin gidan adana kayan tarihi na ” Louvre” inda su ka yi awon gaba da kayayyaki masu daraja.
Ministun harkokin cikin gidan Faransa da na al’adu sun ce; barayin sun dauki mintuna 4 zuwa 7 kadai su ka yi satar.
Da dama daga cikin kafafen watsa labarun kasar ta Faransa sun bayyana abinda ya faru da cewa ya yi kama da abinda ake gani a cikin fina-finai.
Satar dai ta jawo cece-kuce a tsakanin ‘yan siyasar kasar, yayin da kafafen watsa labaru suke yi wa lamarin isgili ta hanyar yin zane-zane.
Jaridar “La Progress” ta amabci cewa a baya ma an taba satar fitaccen zanan “Moniliza” da Leonardo Davinci na kasar Italiya ya zana.”
A wani labarin daga kasar Faransa tsohon shugaban Kasar Nicolay Sarkozi ya fara zaman Kurkuku Na Shekaru 5
A yau Talata ne za a fara kidaya lokacin zaman kurkuku na tsawon shekaru 5 bayan da wata kotu ta same shi da laifin karbar kudaden da ya yi yakin neman zabe daga tsohon shugaban kasar Libya Mu’ammar Kaddafi.
Gabanin shigarsa gidan yarin, Sarkozy ya fada wa jaridar “ La Tribune Dimanche” cewa; Ba na tsoron zaman kurkuku, zan ci gaba da zama cikin izzata.”
An dauki shekaru masu yawa ana yin shari’ar tsohon shugaban kasar ta Faransa, Nicolay Sarkozi bisa zargin da aka yi masa na cewa ya karbi kudaden da ya yi yakin neman zabe da su daga tsohon shugaban kasar Libya Mu’ammar Kaddafi a 2007.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yemen : An yi jana’izar babban hafsan sojin kasar Shahid al-Ghamari a Sana’a October 21, 2025 Iran da Iraki sun bukaci duniya da ta dakatar da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza October 21, 2025 Equatorial Guinea ta zargi Faransa da karan-tsaye wa zaman lafiya a kasar October 21, 2025 Faransa : Sarkozy, ya fara zaman gidan yari na shekara 5 October 21, 2025 Gaza : Falasdinawa 97 sojin Isra’ila suka kashe tun bayan cimma yarjejeniya October 21, 2025 Iran Da Faransa Zasu Yi Musayar Fursinoni, Esfandiari Tana Daga Cikin Wacce Za’a Sallama October 21, 2025 Gaza: Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa 57 A Cikin Sa’o’i 24 Da Suka Gabata October 21, 2025 Kakakin Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Babu Wata Tattaunawa Da HKI October 21, 2025 Tom Barak: Saudiyya na gab da kulla alaka da Isra’ila a hukumance October 21, 2025 Kremlin: Rasha a shirye take don fadada hadin gwiwa da Iran a dukkanin fannoni October 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tsohon shugaban kasar
এছাড়াও পড়ুন:
An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila
Kungiyoyin kare hakkin bil’adama na kasar Canada sun shigar da kara ga jami’an ‘yan sandan kasar, da kuma ma’aikatar shari’a da su kama tsohon Fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Ehud Olmert da kuma ministan harkokin waje Tzipi Livni bisa rawar da su ka taba a baya a laifukan yaki a Gaza a tsakanin 200-2009.
Kungiyoyin sun bukacin ganin an fitar da sammacin kamo ‘yan sahayoniyar biyu a bisa dogaro da dokokin kare hakkin dan’adama da laifukan yaki na kasar Canada, saboda kasar tana karkashin yarjejeniyar Geneva ta 4 da ta bukaci kasashe su hukunta masu irin wadannan laifukan.
Bugu da kari, kungiyoyin sun ce Olmert wanda ya yi fira minista daga 2006 zuwa 2009, shi ne mai rike da mukami na koli a lokacin hare-haren soja da su ka kashe fararen hula da lalata muhimman cibiyoyi. Haka nan kuma a wancan tsakanin sojojin Haramtacciyar kasar Isra’ila sun yi amfani da makamin Phosphorus mai fitar da farin hayaki da aka haramta amfani da shi a yake-yake. Sojojin na mamaya sun kuma rusa gidaje da lalata tsarin magudanan ruwa na kiwon lafiya, kamar kuma yadda su ka yi wa fararen hula da dama kisa ba tare da shari’a ba. Bugu da kari, sun hana shigar da kayan agaji zuwa yankin Gaza a wancan lokacin.
Ita kuwa Livini ta kasance memba a cikin karamar majalisar tsaro wacce ta taka rawa wajen shatawa sojoji ta’asar da su ka yi, ta kuma furta cewa, martanin da ya kamata “Isra’ila” ta mayar wa Falasdinawa ya kamata ya zama ” Na Hauka.”
Dama dai mutanen biyu suna da wata shari’ar da aka kai su kara a gaban kotuna daban-daban na kasashen turai. Kuma a 2009 ne wata kotu a Birtaniya ta fitar da sammaci a kamo su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya December 4, 2025 Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata December 4, 2025 Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe December 4, 2025 MDD ta nemi a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma Tuddan Golan December 4, 2025 Rundunar Ruwa ta IRGC na Gudanar Da Atisayen Soja a Tekun Fasha December 4, 2025 Dan wasan Taekwando Na kasar Iran Ya Samua Lambar Yabo Ta Zinariya December 4, 2025 Hamas Za ta Mikawa Isra’ila Samfurin Da Aka Samu A Karkashin Burabutsai A Gaza December 4, 2025 Iran: Tsaron Yankin Tekun Fasha Jan Layi Ne Da Za’a Fuskanci Mayar Da Martani Adan Aka Taba Shi December 4, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Dan Adam Sun Kira Ga Kasar Kanada Ta Kama Olmert Da Livni December 4, 2025 Majalisa Ta Tabbatar Da Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro December 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci