Tattaunawar wacce aka gudanar a gidan gwamnati dake Kaduna, kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC, da majalisar jihar Kaduna karkashin jagorancin Kwamared Ayuba Suleiman ne ta dauki nauyin gudanar da taron, kuma wakilan kungiyoyin ma’aikatan manyan makarantun ilimi na kwalejin kimiyya da fasaha ta Nuhu Bamalli, Zariya; Kwalejin Ilimi, Gidan Waya; da kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma ta jihar Kaduna dake da cibiyoyin karatu a Kaduna, Kafanchan, da Pambegua, duk sun samu halartar taron.

 

Kungiyoyin sun ayyana daukar wani mataki na yajin aiki ne a ranar 30 ga Satumba, 2025, kan batutuwan da suka shafi aiwatar da tsarin albashi na CONPCASS/CONTEDISS na 2009, fa’idodin ritaya, da jin dadin ma’aikata gaba daya a manyan makarantu mallakar Jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja October 21, 2025 Manyan Labarai An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba October 21, 2025 Manyan Labarai NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi  October 21, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An dawo da malamai 103 da aka kora daga aiki a Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara ta dawo da wasu malamai 103 da aka kora a baya sakamakon binciken tantance ma’aikata tare da biyan su bashin albashin watanni bakwai.

Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na jihar, Malam Wadatau Madawaki, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai kan sakamakon sake nazarin tantance malaman da ma’aikatars ta gudanar.

Madawaki ya ce an cire sunayen waɗannan malamai ne bisa kuskure “ko kuma ta mantuwa” a lokacin gudanar da tantancewar.

“Bayan an kammala tantancewar, mun gano cewa malamai 103 cikin waɗanda aka cire sunayensu an yi kuskure. Sun cancanci kasancewa cikin jerin malamai da aka tabbatar da su,” in ji shi.

Juyin mulki: Ana zargin tsohon gwamnan da ɗaukar nauyin sojojin Najeriya NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?

Kwamishinan ya ce bayan gano kuskuren, ma’aikatar ta rubuta wa Gwamna Dauda Lawal takarda tana neman amincewarsa a dawo da su da kuma a biya su albashin da aka dakatar.

“Daga watan Janairu zuwa Yuli 2025, Ma’aikatar Ilimi, Kimiyya da Fasaha ta rubuta wa Mai Girma Gwamna tana neman ya amince a dawo da waɗannan malamai 103.

“Alhamdulillah, Mai Girma Gwamna ya amince a dawo da su tare da biyan su bashin albashin watan Janairu zuwa Yuli 2025,” in ji Madawaki.

Kwamishinan ya ƙara da cewa gyare-gyaren da ake yi a ɓangaren ilimi na cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na tsaftace tsarin aiki da tabbatar da inganci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo
  • Jihar Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Biliyan Daya Wajen Gyaran Ajujuwa A Makarantu
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni
  • Uba Sani ya yi wa ma’aikatan manyan makarantu ƙarin kashi 70 a albashi
  • Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC
  • Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu
  • NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU
  • An dawo da malamai 103 da aka kora daga aiki a Zamfara
  • Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka