Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso
Published: 23rd, October 2025 GMT
“Allah ya albarkace mu da shugaba mai tsoron Allah da kishin jama’a – mutum ne mai kaunar al’ummar jihar Kano da Nijeriya, kuma me aiki tukuru domin ganin ci gabansu,” in ji Yusuf.
Ya kuma jaddada kudirin sa na ciyar da jihar gaba bisa tsarin falsafar Kwankwasiyya, wanda ke jaddada hidima, rikon amana, da tallafawa.
A nasa jawabin, Kwankwaso ya bukaci ‘ya’yan jam’iyyar NNPP da na Kwankwasiyya na kasa baki daya da su ci gaba da hada kai da kuma jajircewa wajen ci gaban jam’iyyar.
Ya kuma mika godiyarsa ga shugaban NNPP na kasa Dr. Ajuji Ahmed, da sauran shugabannin jam’iyyar daga jihohi sama da 30, da masu biyayya da suka halarci bikin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina
Ya ce tallafin da Shugaba Tinubu ya amince da shi ba rance ba ne, wani bangare ne na yunkurin gwamnati na cire shingen da ke hana ’yan kasuwa ci gaba.
Ya ƙara da cewa gwamnati ta kafa asusun Naira Biliyan 75 da sunan tallafin ga ƙananan masana’antu da yan kasuwa (MSME Intervention Fund), wanda ke bai wa ’yan kasuwa rancen har zuwa Naira miliyan 5 da kaso tara cikin ɗari (9%) a matsayin kudin ruwa, da kuma Naira biliyan 50 a ƙarƙashin shirin Shugaba kasa Bola Tinubu da ke bai wa ƙanana ’yan kasuwa tallafin kuɗi kyauta bisa wasu sharuɗɗa domin bunƙasa kasuwanci (Presidential Conditional Grant Scheme) da ke ba da tallafin Naira 50,000 ga ’yan kasuwa miliyan ɗaya a fadin kasar.
Haka kuma, gwamnatin ta samar da Asusun Tallafin Masana’antu daga Gwamnati (Manufacturers Fund) na Naira biliyan 75 don tallafa wa masana’antu wajen rage tsadar samar da kayayyaki da sufuri.
Mataimakin shugaban ƙasan ya ce sama da ’yan kasuwa 39,000 a jihar Katsina sun amfana da shirye-shiryen gwamnatin tarayya, inda aka raba Naira Biliyan 2.5 a matsayin tallafi da rance mai rangwame.
A ƙarƙashin shirin RAPID, Shettima ya ce ’yan kasuwa 23 daga yankunan karkara sun samu fiye da Naira Miliyan 112 don faɗaɗa kasuwancinsu. Ya kuma yaba wa Gwamna Dikko Raɗɗa bisa kafa KASEDA, yana mai cewa Katsina na zama cibiyar ci gaban masana’antu, noma, da kasuwancin yanar gizo a Arewacin Nijeriya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA