Kazalika, har yanzu batun tsohon shugaban Majalisar Wakilai wato Salisu Buhari, na 1999, na yin amfani da Takardun karatu na bogi da ya yi iƙirarin ya samo daga Jama’iar Toronto, baƙalar na ci gaba da kafa babban misali, a ƙasar.

Badaƙalar ta sa, ba ta tsaya nan ba, ya kuma ƙaryar shekarun na haihauwa, domin kawai, ta tsaya takarar siyasa, a wancan lokacin, wanda kuma ya nuna turjiya daga sauka daga muƙamin na nsa duk da ɗimbin hujjojin da suka bayyana a kansa, inda bayan komai ya bayyana ƙarara, ya sauka daga kan muƙamin shugabancin Majlisar a 2000, ya kuma ɓarke da kuka a Majalisar, ya amsa cewar, Takardunsa na bogi ne.

Haka ita ma, tsohuwar ministan kuɗi Kemi Adeosun, aka samu hanunta dumu-dumu a cikin irin wannan ɗabi’ar ta aikta badaƙala, bayan an gao cewa, Takardar ta neman tsame ta daga yi wa ƙasa hidima, ta bugi ce.

Haka zalika, aikata irin wannan badaƙalar ta kwana-kwanan ita ce ta ministan ƙirere, kimiyya da fasaha wato Uche Nnaji, wanda shi ma, ya gabarwa da shugaban ƙasa Takardun karatunsa na bogi, da ya yi iƙirarin ya samo daga jami’ar Nsukka, domin a tantance shi, ya zama ministan wannan ma’aikatar.

Wannan badaƙalar, za iya cewa, kusan ta faro ne, tun a cikin Azuwan makaranta wanda hakan ya nuna cewa, ba daga kan ‘yan siya ta samu asali ba, inda masu sanya ido kan ɗaliban da ke kan zana jarrabawa, inda masu sanya idon, ke yiwa wasu ɗaliaban jigar Takardun satar amsar jarrabawa.

Hakazalika, lamarin ya kuma nuna jadda wasu iyayen ke haƙilon ganin ‘ya’yansu, sun zana jarrabar kammala sakandare a cibiyon zama jarrabawa, na neman na neman sa’a, domin kawai ‘ya’yansu, su lashe jarrabawar.

Akwai kuma batun yadda ake sauya samakaon jarrabawa yayin kwafo sakamakon WAEC ta hanyar haɗa baki, da wau gurɓatattun ma;aikata a ma’aikatun ilimi da kuma bayanan shidar karatun mutum wato CƁ da Takarun bogi na NYSC.

Irin wannan lamarin, ya kuma haifar da samun wasu matasan ƙasar na shiga cikin mummunar ɗabi’ar damfara ta kafar Internet, wato waɗanda ake yiwa laƙabi da, ‘Yan Yahoo-Yahoo”, inda suka damfarar mutane miliyoyin kuɗaɗe, ta nahyar yin kutse a cikin Asusun ajiarsu na Bankuna.

Lamarin na kuma sanya wasu ma’aikatan Gwamnati da wasu sanatoci, yin arigizo a cikin kasafin kuɗi da kuma biyan wasu ‘yan kwangila kuɗaɗen yin kwangila wanda daga baya, su yi watsi, da aikin, bayan sun karbi kuɗin yin kwagilar.

Abin dubi a nan shi ne, idan har masu aikata irin ɗabi’ar za su iya wucewa da tunanin manyan hukumomin ƙasar wajen yin amfani da Takardun karatu na bogi, kamarsu, majalisar dattawa ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya DSS, hakan ya nuna ƙarara, orin gazarwar waɗannan hukumomin, musamman duba da yadda minista sukutum ya miƙa gabatar da Takardun karatu na bogi, domin a tantance shi a muƙamin minista. 

A ra’ayin wannan Jaridar, ya zama wajibi, wannan lamarin, ya sama na ƙarshe da wasu ke aikata wa a ƙasar kuma ya zama wajibi, majalsar ƙasar ta tabbatar ana gudanar da cikakken bincike a ɗaukacin mayan makarantun ƙasar da kuma samo sahihan bayanai na ministocin da ke kan muƙamasu da shuwagannin hukumomin Gwamnati da kuma na ‘yan majalisar da suka samu Takardun sheda na NYSC.

Bugu da ƙari, jami’oin ƙasar da kuma mahukaunata  a NYSC, su rinƙa yin amfani da sahihiyar kafar intanet da aka aminta da ita, wajen wallafa sunayen wa rijista.

Kazalika, ya zama wajibi, a rinƙa hukunta duk ɗan ƙasar da aka same shi, da aikata wannan mummunar ɗabi;ar domin hakan ya zama izina, ga sauran masu tunanin aikata hakan, a gaba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno October 23, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC October 23, 2025 Manyan Labarai Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna October 23, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da Takardun

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

Manzon Allah (S.A.W.) yana da tunani mai zurfi, tunanin nan har ya shigar da shi duniyar tunani, duniyar tunani ta zamar masa gaskiya har yana tu’ammali da duniyar tunani, in ji mai wannan littafin masanin falsafa. Manzon Allah (S.A.W.) cikin gaskiya ya shiga ya yi tafakkuri, ya ya ibada, ya yi zikiri har ya koma asalinsa har ya haɗu da haƙiƙarsa ta Muhammadiyya (S.A.W.). Wata rana Annabi yana sallah a nan inda yake da Sahabbai, ya ce ga Al’janna ina kallo ga kuma wuta nan ina kallo, kai dai ba ka ji zafinta ba.

Manzon Allah (.S.A.W.) yana da tunani mai zurfi, yana da yalwar tunani da ƙarfi, kai har abin da ƙwaƙwalwarsa take shirya masa sai ya zama gaskiya, gashi yana gani, in ƙarya ne ya za a yi a gani, a’a wannan gaske ne dama ana haka, kuma mumini a imaninsa idan ya yi imani aljannar nan sai ya ganta tun daga nan duniya, Allah ya kiyaye idan wuta ce sai ya ganta tun a nan, idan mala’iku ne sai ya gan su, duk ba wani abu ba ne zai iya ganin su tun daga nan duniya, ko Annabi ne zai iya ganin shi tun daga nan duniya. Wannan duniyar nan ga baki ɗaya wani ɗigo ne a cikin wannan duniyar ta tunani, ita ma wannan duniyar ta tunani ɗan ɗigo ce a cikin duniyar haƙiƙa.

Mafalsafin nan yake cewa Manzon Allah (S.A.W.) mutum ne mai ɗaukaka da tsarki da ya kai kowane irin matsayi na mai girma (S.A.W.), don haka wata wuya ko wani bala’i bai jin sa, ba wai bai jin sa a haƙiƙa ba ko ya dame shi ba, yana ji amma abin da yake so ya kai ya hana shi jin zafin wannan bala’i.

Manzon Allah yana da ƙarfin hankali wanda ya fi ƙarfin misaltuwa, yana da ƙarfin hankali, sannan yana da ƙarfin haƙuri, abin da zai samu wani gwarzon ya yi raki da ihu, amma Manzon Allah (S.A.W.) sai a yi a gama ba ka san an yi ba. Yana da ƙarfin niyya kamar yadda ya fara faɗa a farko.

Yake cewa ko ka ji an ce yana da wasu abubuwa, ba ana nufin laifi ba ne mai sunan laifi, a’a wani hali ne ya kawo dole ya yi wannan abun, ko kai ne ka zama shugaban jama’a dole ka yi wannan abin, yake cewa dole ce ta kawo, masalaha ce ta kawo kasancewarsa shugaba, kasancewarsa shugaba kuma jagora, ta sa dole sai ya yi wannan, ashe idan da adalci ba za ka kama shi da wannan laifi ba, amma a wajen mai wannan abu laifi ne, ka ga Sayyadina Ali shi ne ya yi irin wannan, ai a yanayin gudanar da mulki dole akwai tsarin da sai an buge shi, ka ga kamar a hukuncin da aka yanke wa Bani Ƙuraiza suka ce a tafi kotun Attaura, wannan hukuncin da ya bi hukuncin Attaura ne, kuma ba Manzon Allah ne ya yi wannan hukunci ba Sa’ad bin Muaz ne ya yi, Manzon Allah (SAW) kuma ya zartar, maslaha ce ta kawo kasancewarshi shugaba, ka ga idan da adalci ba za ka kama shi da wannan ba.

Bafalsafin, yake cewa Manzon Allah (S.A.W.) ya ci nasara wajen zaburar da al’ummarsa, wannan canza al’umma da ya yi, wanna juyi da ya kawo wa al’umma shi ne ya tabbata har yau. Manzon Allah (S.A.W.) bai yi shekara talatin (30) da rasuwa ba sai da mulkin al’ummarsa na larabawa ya kama tun daga Pakistan har ya zuwa Danja, duk mulkinsu ne gaba ɗaya, kuma su mutanen waɗannan wurare duk sun yarda da karatunsa, sun yarda da iliminsa, saboda Allah Ya tsarkake shi, kuma ya sa shi abin bi ne, (S.A.W.) Allah ya tabbatar  da ambatonsa a cikin duk wasu shugabanni da aka yi masu tsarki. 

Manzon Allah ya taɓa tambayar Jibril (A.S.) me ake nufi da “Wa rafa’ana laka zikirak”sai Jibri (A.S.) ya ce ya tambayo masa, sai ya ce abin da ake nufi shi ne duk lokacin da aka ambaci sunan Allah sai an ambace ka cikin Sallah da cikin ambatonsa da sauransu, saboda (Manzon Allah) ya ƙare cikin Halarar Allah, saboda matsayin da ya kai (S.A.W).

Imamu Zuhuri, (malamin hadisi ne), yana cikn salafus salihin, yake cewa da mutum zai yanka saniya ko ya yanka rago ko kaza da sunan Manzon Allah (S.A.W.) ya halatta a ci, saboda me, saboda Ubangiji ya ce “Wa rafa’ana laka zikirak” ya kawo ambatonsa a wajen, amma in da irin shuwagabanninmu ne na nan sai su ce Haram. Amma sun ce da kirista zai iya yin yanka musulmi ya ci, Allah ya ce abincinsu halal ne a wajenmu, mu ma namu halal ne a wurinsu, sai dai ban da giya da alade da Allah ya haramta (don babu wani abinci na alade da za a kawo ka ci), ka ga bambancin karatun malamai na baya da na yanzu, na baya suna da zurfin tunani.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano October 24, 2025 Manyan Labarai Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu October 24, 2025 Manyan Labarai Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba October 24, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala
  • Shugaba Tinubu Ya Jaddada Kudurin Gwamnatinsa Na Ƙara Zuba Jari A Ilimi
  • NAJERIYA A YAU: Me Dawowar Hare-hare Kan Sojoji Ke Nufi A Arewa Maso Gabas?
  • Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno
  • Kwamishinan Ilimi Na Kano Ya Yi Kira Da A Karfafa Shugabancin Makarantu Domin Inganta Karatun Dalibai
  • Ko Alassane Ouattara zai samu wa’adi na 4 a mulkin Ivory Coast?
  • Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi
  • Uba Sani ya yi wa ma’aikatan manyan makarantu ƙarin kashi 70 a albashi