Aminiya:
2025-10-20@17:05:00 GMT

Gwamnonin Kano, Katsina da Jigawa sun ƙulla yarjejeniyar bunƙasa wutar lantarki

Published: 20th, October 2025 GMT

Gwamnonin Kano da Katsina da na Jigawa sun shiga wata yarjejeniyar haɗin gwiwa kan bunƙasa kasuwar wutar lantarkin jihohin uku.

Wannan na zuwa ne bayan gwamnonin sun zuba hannun jari a kamfanin Future Energies Africa (FEA), babban mai zuba jari a kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano wato KEDCO.

Kano Pillars ta dakatar da Kocinta An kama ɗan uwan Nnamdi Kanu da lauyansa —Sowore

A cewar wata sanarwa da Kwamishinan Wutar Lantarki da Makamashi na Jihar Kano, Dokta Gaddafi Sani Shehu, ya fitar, an cimma yarjejeniyar ne a yayin taron bunƙasa wutar lantarki da aka gudanar a birnin Marrakech, Morocco, daga ranar 16 zuwa 19 ga Oktoba, 2025.

Dokta Gaddafi ya bayyana cewa jihohin uku za su yi aiki tare wajen gano sabbin hanyoyin inganta kasuwannin wutar lantarki, tare da kafa tsare-tsaren doka da tsarin haɗin gwiwa don inganta aikin rarrabawa da samar da wuta.

Ya ce, “samun hannun jari a kamfanin FEA zai taimaka wajen ƙarfafa dabarun KEDCO da kuma bunƙasa samar da wutar lantarki a yankin Arewacin Yamma.”

Kwamishinan ya ƙara da cewa jihohin za su kashe naira biliyan 50 wajen aiwatar da ayyukan bunƙasa wutar lantarki da kuma samar da wuta ta hanyoyi daban-daban, ciki har da na tsarin amfani da fasahar samar da wuta da hasken rana.

“Kazalika, za mu yi aiki tare da KEDCO domin rage asarar wuta daga masu amfani a gida, wanda hakan zai taimaka wajen tabbatar da ingantaccen samar da wuta ga al’umma,” in ji shi.

An tsara cewa wakilan jihohin za su gudanar da taron kasa da kasa a kowace shekara, sannan su gana sau huɗu a shekara domin duba ci gaban ayyuka da tsara manufofi da karfafa dangantaka a kasuwar wutar lantarki ta jihohi uku.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dikko Umar Radda Jihar Jigawa Jihar Kano Jihar Katsina wutar lantarki samar da wuta

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

 

Gwamna Radda ya jaddada cewa hukumomin tsaro kadai ba za su iya fada da ‘yan ta’adda ba, sai dai da gudummuwar ‘yan kasa. Ya yi kira ga ‘yan Nijeria da su zama masu sanya ido da kai rahotanni cikin gaggawa da bayar da ingantattun bayanai ga jami’an tsaro.

 

Ya yaba wa gwamnatin Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu bisa inganta tsaro da maido da martabar tattalin arzikin kasar nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi October 18, 2025 Labarai Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF October 18, 2025 Labarai Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili October 18, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Nemi Alkalai Su Kara Kaimi Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa
  • ShTinubu Ya Nemi Alkalai Su Kara Kaimi Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa
  • Isra’ila Ta Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta Sau 80 Ta Kashe Mutane 97 Ta Jikkata 230
  • Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
  • Hamas ta yi Allah wadai da Isra’ila kan keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta
  • Jihar Jigawa Za Ta Gina Tashoshin Samar Da Ruwan Sha Masu Amfani Da Hasken Rana
  • Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul
  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro
  • Gwamnonin APC sun yi taro a Jihar Kebbi