Gwamnonin Kano, Katsina da Jigawa sun ƙulla yarjejeniyar bunƙasa wutar lantarki
Published: 20th, October 2025 GMT
Gwamnonin Kano da Katsina da na Jigawa sun shiga wata yarjejeniyar haɗin gwiwa kan bunƙasa kasuwar wutar lantarkin jihohin uku.
Wannan na zuwa ne bayan gwamnonin sun zuba hannun jari a kamfanin Future Energies Africa (FEA), babban mai zuba jari a kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano wato KEDCO.
Kano Pillars ta dakatar da Kocinta An kama ɗan uwan Nnamdi Kanu da lauyansa —SoworeA cewar wata sanarwa da Kwamishinan Wutar Lantarki da Makamashi na Jihar Kano, Dokta Gaddafi Sani Shehu, ya fitar, an cimma yarjejeniyar ne a yayin taron bunƙasa wutar lantarki da aka gudanar a birnin Marrakech, Morocco, daga ranar 16 zuwa 19 ga Oktoba, 2025.
Dokta Gaddafi ya bayyana cewa jihohin uku za su yi aiki tare wajen gano sabbin hanyoyin inganta kasuwannin wutar lantarki, tare da kafa tsare-tsaren doka da tsarin haɗin gwiwa don inganta aikin rarrabawa da samar da wuta.
Ya ce, “samun hannun jari a kamfanin FEA zai taimaka wajen ƙarfafa dabarun KEDCO da kuma bunƙasa samar da wutar lantarki a yankin Arewacin Yamma.”
Kwamishinan ya ƙara da cewa jihohin za su kashe naira biliyan 50 wajen aiwatar da ayyukan bunƙasa wutar lantarki da kuma samar da wuta ta hanyoyi daban-daban, ciki har da na tsarin amfani da fasahar samar da wuta da hasken rana.
“Kazalika, za mu yi aiki tare da KEDCO domin rage asarar wuta daga masu amfani a gida, wanda hakan zai taimaka wajen tabbatar da ingantaccen samar da wuta ga al’umma,” in ji shi.
An tsara cewa wakilan jihohin za su gudanar da taron kasa da kasa a kowace shekara, sannan su gana sau huɗu a shekara domin duba ci gaban ayyuka da tsara manufofi da karfafa dangantaka a kasuwar wutar lantarki ta jihohi uku.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dikko Umar Radda Jihar Jigawa Jihar Kano Jihar Katsina wutar lantarki samar da wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatinsa na shirin sayen jirage marasa matuƙa da wasu kayan aiki domin kare yankunan da ke iyakar Kano da Katsina.
Kakakin gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.
Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000Gwamna Abba, ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci sansanin rundunar haɗin gwiwa ta JTF, domin ganin yadda suke shirin kare al’umma daga hare-haren ’yan bindiga a yankunan Tsanyawa da Shanono.
Ya roƙi al’ummar yankunan da abin ya shafa da su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani game da duk wani motsi na ’yan bindiga.
Gwamnan ya ce ya kai wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ziyara, domin neman taimako kan lamarin, inda shugaban ya amince da buƙatar da aka gabatar masa cikin gaggawa.
Ya umarci dakarun JTF da su yi duk mai yiwuwa wajen ceto mutanen da aka sace a Tsanyawa da Shanono.
“Mun san cewa waɗannan hare-hare sun jawo asarar rayuka, wasu kuma an yi garkuwa da su. Insha Allah za a ceto su,” in ji shi.
Gwamna Abba ya ce sun kai wannan ziyara ne domin fahimtar halin tsaron yankin da kuma ƙarfafa guiwar jami’an tsaro.
Ya ƙara da cewa irin wannan matsalar tsaro sabon abu ne a Kano, amma gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro domin magance ta.
A yayin ziyarar, ya jajanta wa iyalan mutanen da aka sace tare da tabbatar musu cewa gwamnati na ƙoƙarin ganin an dawo da su cikin gaggawa.
Rahotanni sun nuna cewa aƙalla mutum 10 aka sace a Tsanyawa da Shanono, ciki har da wata tsohuwa da ’yan bindiga suka hallaka.