Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-24@11:40:31 GMT

Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano

Published: 24th, October 2025 GMT

Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano

Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa gobara ta lalata rumfuna 529 daga cikin rumfuna na wucin gadi a Kasuwar Shuwaki da ke ƙaramar hukumar Gari, Jihar Kano.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar, Alhaji Saminu Abdullahi, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Kano.

A cewarsa, hukumar ta samu kiran gaggawa misalin ƙarfe 3:25 na rana daga Abdulmalik Muhammad na ofishin kashe gobara na Gari, yana sanar da aukuwar gobara a kasuwar.

Ya bayyana cewa, da zarar sun samu bayanin, hukumar ta aika jami’ai da motocin kashe gobara zuwa wurin domin kashe wutar tare da hana ta yaduwa zuwa sauran sassan kasuwar.

Saminu ya ce yankin kasuwar yana da fadin kimanin kafa 3,000 da 2,500, kuma yana ɗauke da kusan rumfuna 1,000 na wucin gadi, inda rumfuna 529 suka ƙone ƙurmus.

Sai dai ya tabbatar cewa ba a rasa rai ba a wannan hatsari.

Ya danganta musabbabin gobarar da aikace-aikacen wasu mutane masu shaye-shaye da ke zaune a cikin kasuwar.

Mai magana da yawun hukumar ya shawarci jama’a da ’yan kasuwa da su kasance masu hankali da taka-tsantsan wajen amfani da wuta da abubuwan da ke iya kama da wuta, domin kauce wa irin wannan ibtila’i a nan gaba.

Khadijah Aliyu

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gibara Kano kashe gobara

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe manoma uku da suke girbin amfanin gona a Filato

Wasu ’yan bindiga sun kai hari kan manoman da suke aikin girbin amfanin gona a yankin Mbor na masarautar Mushere na Ƙaramar hukumar Bokkos a Jihar Filato, inda suka kashe mutane uku tare da jikkata wasu biyu a ranar Laraba da yamma.

Shugaban Ƙungiyar matasan Mushere, Kopmut Monday ne ya tabbatar wa Daily Trust faruwar lamarin a ranar Alhamis.

Boko Haram sun kai sabbin hare-hare a wasu yankunan Borno da Yobe Jami’an tsaro sun kama Sowore saboda shirya zanga-zanga

A cewar shugaban matasan, ’yan bindigar sun kai farmaki wurin ne inda suka buɗe wuta kan manoman da ke cikin aikin girbin amfanin gona, inda ya ce manoman sun tsere domin tsira da rayukansu.

Shugaban ya zargi makiyaya da kai wa mambobinsu hari, inda ya bayyana cewa, waɗanda ake zargin “mazauna garin Rongjing ne a jiya da yamma sun kai wa ’yan ƙungiyarmu hari a yankin Mbor a lokacin da suke girbin amfanin gona, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane uku da jikkata mutum biyu da harbin bindiga. Waɗanda suka jikkata na cikin mawuyacin hali.

Monday yya ƙara da cewa, al’ummar yankin suka sha fama da irin wannan hari a ranar 26 ga watan Mayu an kashe mutane bakwai.

Ya ce “lamarin baya-bayan nan wani mummunan al’amari da ya faru a watan Mayu, wanda ya yi sanadin kisan mutane bakwai, da jikkata wasu da kuma ƙona gidaje da dama ciki har da coci guda biyu.”

Monday ya kuma bayyana cewa, al’ummar da aka kai wa harin baya-bayan nan, sun yi kira ga jami’an tsaro da su tura isassun ma’aikata don dawo da zaman lafiya a yankin saboda mazauna yankin ba za su iya gudanar da harkokinsu na yau da kullum ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • AGILE Kano Ta Tattauna da Malamai da Limamai Don Ƙarfafa Goyon Bayan Ilimin ’Yan Mata
  • Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Karfafa Dangantaka Da NAFDAC
  • An kashe manoma uku da suke girbin amfanin gona a Filato
  • MTN zai rufe ofisoshi 101 a Kano, Borno da Adamawa saboda gyare-gyare
  • Labarin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Najeriya ƙarya ne – Sarkin Musulmi
  • Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
  • Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya
  • Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsa