Gobara Ta Ƙone Fiye da Rumbuna 500 a Kasuwar Kano
Published: 24th, October 2025 GMT
Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa gobara ta lalata rumfuna 529 daga cikin rumfuna na wucin gadi a Kasuwar Shuwaki da ke ƙaramar hukumar Gari, Jihar Kano.
Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar, Alhaji Saminu Abdullahi, ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Kano.
A cewarsa, hukumar ta samu kiran gaggawa misalin ƙarfe 3:25 na rana daga Abdulmalik Muhammad na ofishin kashe gobara na Gari, yana sanar da aukuwar gobara a kasuwar.
Ya bayyana cewa, da zarar sun samu bayanin, hukumar ta aika jami’ai da motocin kashe gobara zuwa wurin domin kashe wutar tare da hana ta yaduwa zuwa sauran sassan kasuwar.
Saminu ya ce yankin kasuwar yana da fadin kimanin kafa 3,000 da 2,500, kuma yana ɗauke da kusan rumfuna 1,000 na wucin gadi, inda rumfuna 529 suka ƙone ƙurmus.
Sai dai ya tabbatar cewa ba a rasa rai ba a wannan hatsari.
Ya danganta musabbabin gobarar da aikace-aikacen wasu mutane masu shaye-shaye da ke zaune a cikin kasuwar.
Mai magana da yawun hukumar ya shawarci jama’a da ’yan kasuwa da su kasance masu hankali da taka-tsantsan wajen amfani da wuta da abubuwan da ke iya kama da wuta, domin kauce wa irin wannan ibtila’i a nan gaba.
Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gibara Kano kashe gobara
এছাড়াও পড়ুন:
Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
Hukumar Kwastam, ta kama kilo 25.5 na hodar iblis a wani jirgin ruwa na ƙasar Brazil mai suna MV San Anthonio a tashar jirgin ruwa ta Legas.
An ɓoye hodar cikin ƙananan jakunkuna biyar.
’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —GwamnatiKwanturola Emmanuel Oshoba, ya ce an gudanar da aikin ne bayan samun bayanan sirri tare da haɗin gwiwar hukumar NDLEA.
Ya ƙara da cewa jirgin ya tsaya a ƙasashen da suka yi ƙaurin suna wajen harkar safarar miyagun ƙwayoyi kafin isowarsa Najeriya.
An tsare jirgin, sannan an miƙa hodar da aka kama ga NDLEA domin ci gaba da bincike.
Oshoba, ya ce wannan nasara tana nuna jajircewar hukumar Kwastam wajen kawar da haramtattun kasuwanci da kuma kare ƙasa, musamman lokacin bukukuwan ƙarshen shekara ke ƙaratowa.
Ya yi gargaɗin cewa hukumar ba za ta bari a yi amfani da ita wajen aikata laifuka ba, kuma duk kayayyakin da suka shigo da su sai an yi bincike a kansu.
A cewarsa, haɗin kai tsakanin Kwastam da NDLEA yana bayar da kyakkyawan sakamako, kuma zai ci gaba da karya tsarin masu safarar miyagun ƙwayoyi.
Jami’an NDLEA ƙarƙashin jagorancin CN Haliru Umar sun karɓi kayan da aka kama.
Kwastam ta kuma buƙaci masu mu’amala da tashar su kasance masu bin doka tare da kai rahoton duk wani abun zargi domin tabbatar da tsaron tashar.