Asusun Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya tabbatar da aniyarsa ta inganta daidaito tsakanin maza da mata da kuma karfafa jagorancin mata a fannin ilimi a Jihar Jigawa.

Shugabar Ofishin UNICEF na Kano, Rahama Rihood Mohammed, ya bayyana hakan a wani taron da HiLWA ta shirya tare da tallafin Kungiyar Tarayyar Turai (EU) a Dakin Taro na Manpower Development Institute.

Ya ce bincike ya nuna cewa ko da yake mata su ne mafi rinjaye a aikin koyarwa a Jigawa, suna da kaso 14 bisa 100 ne kacal a mukaman shugabanci, kamar shugabar makaranta ko mataimakiya. Wannan, a cewarsa, yana takaita gudunmawar mata wajen tsara manufofi da ci gaban ilimi.

Rahama Ya bayyana cewa matsalolin al’adu, tsarin aiki, da rashin damar samun jagoranci na hana mata ci gaba, yana mai cewa idan mata suka jagoranci makarantu, ana samun kyakkyawar gudanarwa da karin nasara ga dalibai, musamman ‘yaya mata.

Ya ce a karkashin Shirin Jinsi na UNICEF (2022–2025), za a ci gaba da dakile matsalolin da ke hana mata cigaba, samar da tsarin daukar aiki da karin girma bisa adalci, da kuma gina hanyoyin koyarwa ga mata masu neman mukaman shugabanci.

UNICEF ya jaddada cewa zai ci gaba da aiki tare da HiLWA, da  EU, da Gwamnatin Jigawa domin samar da manufofi da za su karfafa mata a harkar ilimi.

Ya ce karfafa jagorancin mata ba  batun adalci ba ne kadai, muhimmin mataki ne na gina kyakkyawar makomar yara.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Wasu direbobi sun bayyana cewa tsarin ya taimaka wajen tabbatar da tsaro, ko da yake  fyana jinkirta tafiya.

Wasu kuma sun ce farashin sufuri ya ɗan ƙaru sakamakon sabon tsarin.

Mutane da ƙungiyoyin farar hula sun yaba da nasarar, amma sun buƙaci gwamnati ta tabbatar da cewa yaran da aka ceto sun samu kulawa, ilimi, da sake gana su da iyayensu.

Dakta Sabo ya ce hukumar sufuri za ta ci gaba da haɗa kai da jami’an tsaro tare da faɗaɗa ayyukanta domin tallafa wa tattalin arziƙin jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara October 20, 2025 Manyan Labarai Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a October 20, 2025 Manyan Labarai ‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta October 20, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha da Habasha sun tattauna kan karfafa hadin gwiwa a tsakaninsu a fannin nukiliya
  • Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya
  • Yadda Kwankwaso ya yi murnar zagayowar ranar haihuwarsa
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Hanya Akan Kudi Sama Da Naira Biliyan 4
  • Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu
  • Muna Samun Gagarumin Cigaba Wajen Dawo Da Zaman Lafiya A Zamfara-Gwamna Lawal
  • APC ta rage wa Mata kuɗin tsayawa takara a Borno
  • SUBEB Ta Gudanar Da Jarabawa Ga Malaman Da Ke Neman Mukaman Sakatarorin Ilimi A Jigawa
  • Dakarun kare Juyin Musulunci Na Iran Sun Bayyan Shirinsu Na Karfafa Dabarun Hadin Guiwa Da yamen