Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027
Published: 24th, October 2025 GMT
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, a ranar Alhamis, ya rantsar da Farfesa Joash Ojo Amupitan (SAN), a matsayin sabon shugaban Hukumar Zabe ta Ƙasa (INEC) na shida da aka tabbatar da shi.
An gudanar da wannan gajeren bikin rantsarwa ne a ɗakin taro na fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.
NAJERIYA A YAU: Me Dawowar Hare-hare Kan Sojoji Ke Nufi A Arewa Maso Gabas? An kashe manoma uku da suke girbin amfanin gona a FilatoBayan rantsarwar, Shugaba Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC da ya yi aiki da gaskiya da amana, ba tare da wata matsala ba.
“Naɗa ka da kuma tabbatar da kai da Majalisar Dattawa ta yi, alama ce ta ƙwarewarka da amincewar da bangarorin zartaswa da na dokoki suka nuna gare ka.
“Wannan babbar nasara alama ce ta fara tafiya mai ƙalubale amma mai albarka, kuma ina da tabbacin za ka ɗauki wannan nauyi da cikakkiyar gaskiya, sadaukarwa da ƙaunar ƙasa,” in ji Shugaba Tinubu.
Shugaban ƙasa ya bayyana cewa Najeriya ta fara tafarkin dimokuraɗiyya tun daga 1999, tare da ci gaba mai ma’ana wajen ƙarfafa hukumomi da tsare-tsare, inda ya ce: “Dimokuraɗiyyar mu ta yi nisa cikin shekaru 25. Mun ƙarfafa hukumomin dimokuraɗiyya, musamman tsarin zabe, ta hanyar kirkire-kirkire da gyare-gyare.
“Muna ci gaba da koyon darussa, kuma mun inganta sosai fiye da yadda muke shekaru da suka wuce. Yanzu dole ne mu ci gaba da bin ƙa’idojin dimokuraɗiyya a cikin al’umma mai rikitarwa da sassa da dama.
“Tsarin zabe muhimmin ɓangare ne na dimokuraɗiyya wanda ke ba jama’a damar zaɓar shugabanninsu da tsara makomarsu. Don tabbatar da ci gaban dimokuraɗiyya, dole ne a tabbatar da ingancin tsarin zabe,” in ji shugaban.
Tinubu ya ce zaben gwamna da za a gudanar a Jihar Anambra a ranar 8 ga Nuwamba, 2025, zai zama zakaran gwajin dafin jagorancin sabuwar hukumar zabe.
“Yana da matuƙar muhimmanci a tabbatar da cewa zabukanmu suna da kyau, adalci da inganci. Dole ne mu ci gaba da inganta tsarin zabe, mu magance matsalolin da suka gabata, mu kuma kawo sabbin hanyoyi don yau da gobe.
“Babu tsarin zaben da ba shi da matsala, amma tun da zabe muhimmin ginshiƙi ne ga makomar ƙasa, dole ne a ci gaba da ƙarfafa hukumomin zabe, a tabbatar da cewa suna da ƙarfi, juriya, kuma an kare su daga matsalolin da za a iya kauce wa.
“Saboda haka, ina ba ka umarni, Farfesa Amupitan, yayin da ka ɗauki wannan nauyi mai muhimmanci, da ka kare ingancin tsarin zabukanmu, da kuma ƙarfafa ƙarfin hukumar INEC.”
Bikin rantsarwa ya biyo bayan tabbatar da naɗa Amupitan da majalisar dattawa ta yi a ranar 16 ga Oktoba.
Amupitan ya gaji Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya jagoranci INEC daga 2015 zuwa 2025.
Da yake jawabi ga ’yan jarida bayan bikin, sabon shugaban na INEC ya yi alkawarin kare kundin tsarin mulki da dokokin Najeriya dangane da tsarin zabe.
Ya kuma yi alkawarin yin aiki tare da masu ruwa da tsaki don nasarar zabe a ƙasa.
Ya ce, “Zan kare kundin tsarin mulki da dokokin Najeriya dangane da tsarin zabe, kuma kamar yadda Shugaban Ƙasa ya ce, an ba ni umarni kai tsaye da na tabbatar da zabe mai inganci, adalci da nagarta.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: a tabbatar da tsarin zabe
এছাড়াও পড়ুন:
Tun da PDP ta bar mulkin Najeriya maguɗin zaɓe ya ragu – Akpabio
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce tsarin zabe a Najeriya ya samu gagarumin ci gaba tun bayan da jam’iyyar PDP ta bar mulkin kasar a matakin tarayya.
Akpabio, wanda aka zabe shi sau biyu a matsayin gwamna karkashin PDP kuma ya fara shiga majalisar dattawa a karkashin jam’iyyar, ya bayyana hakan ne a lokacin karatu na biyu a kan dokar gyaran tsarin zabe a zaman majalisa da aka yi a ranar Laraba.
Dangote zai sayar da kaso 10 na hannun jarin matatar man shi NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Haraji Da Zai Fara Aiki A 2026“Ina da tabbacin cewa ni da Sanata Abaribe, wanda muka shafe kusan shekaru 25 muna cikin harkar siyasa, na san ba mu damu da jam’iyya ba, ana iya lashe zabe a ko’ina.
“Ka na da ƙwarewa sosai, amma za ka yarda da ni cewa tun bayan faduwar PDP, zabe ya inganta matuka a wannan ƙasa.
“Na tuna, ina da kusanci da yawancin shugabannin ƙasa tun daga 1999, kuma a 2007 lokacin da na ci zabe a matsayin gwamna, shugaban ƙasa na lokacin, Allah ya jiƙansa, Shugaba Yar’Adua, ya fito fili ya ce zaben da ya kawo shi mulki yana da lam’a.
“Ya ce cike yake da kura-kurai da magudi. Tun daga lokacin, muka fara rufe guraben da ke haifar da matsala.”
Akpabio ya ƙara da cewa duk da cewa ’yan Najeriya na fuskantar ƙalubale, tsarin ya inganta.
“Ka duba zaben da ya gabata, har sai da muka je Kotun Koli muna muhawara kan ko lashe babban birnin tarayya kadai ya isa ya sa dan takara ya zama shugaban ƙasa,” in ji shi.
“Hankali kawai ya isa ya gaya mana cewa ba haka dokar zabe take nufi ba,” in ji Akpabio.
Shugaban majalisar dattawa ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki bayan PDP ta fadi zabe a shekarar 2015.
Ya tsaya takarar Sanata a 2019 a karkashin jam’iyyar APC, amma bai ci ba.
Sai dai tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya naɗa shi minista daga bisani, kafin a 2023 kuma ya ci zaben sanatan daga jiharsa ta Akwa Ibom, sannan aka zabe shi shugabancin majalisar.