Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta bayyana cewa matasa dubu ɗaya (1,000) za su samu horo kan tsaron yanar gizo (cyber security) da fasahar binciken dijital (digital forensics) ta hanyar Cibiyoyin Koyon Fasahar Dijital ƙarƙashin Shirin Renewed Hope Initiative (RHI) a Jihar Nasarawa.

Uwargidan Shugaban Ƙasan ta bayyana haka ne yayin bikin kaddamarwa da miƙa Cibiyar Koyon Fasahar Dijital (Digital Learning Center) a Lafia da wasu jihohin ƙasar.

Sanata Oluremi Tinubu ta ce, shirin horon matasan wanda za a rika gudanarwa a kowane mako daga yanzu har zuwa watan Disamba na shekara mai zuwa, yana da nufin yakki da laifukan yanar gizo (cyber crimes) da kuma ƙarfafa matasa su samu ƙwarewa ta yadda za su dogara da kansu a rayuwa.

Uwargidan Shugaban Ƙasan ta yaba wa Daraktan Hukumar NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, bisa ƙoƙarin gina cibiyoyi 15 na koyon fasahar dijital tare da haɗin gwiwar Renewed Hope Initiative, domin bunƙasa damar samun ilimi ta fasahar zamani a ƙasar.

A nasa jawabin, Daraktan Janar na NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, ya bayyana cewa dijitalizashan (digitalization) muhimmin ginshiƙi ne a cikin manufofin sauyin gwamnati ta yanzu, don haka aka kafa cibiyoyi 296 na koyon fasahar dijital a fadin ƙasar.

Ya ƙara da cewa a bana, NITDA tana shirin ƙara cibiyoyi 148, wanda hakan zai kai adadin cibiyoyi zuwa 586 kafin shekarar 2027.

Shi ma Daraktan Janar na Hukumar Fasahar Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital ta Jihar Nasarawa (NASITDA), Sani Haruna Sani, ya bayyana cewa wannan cibiya za ta zama hedikwatar horo kan ilimin dijital, tsaron yanar gizo da kuma binciken forensics a jihar.

Ya yi kira ga matasan jihar da su amfana da wannan dama domin su ƙara kwarewa a fannin fasahar zamani, su taimaka wajen ci gaban tattalin arzikin jihar da ƙasa baki ɗaya.

Aliyu Muraki, Lafia

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: nasarawa fasahar dijital

এছাড়াও পড়ুন:

Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno

Wata nakiya da ta fashe a garin Banki, da ke Ƙaramar Hukumar Bama, a Jihar Borno, ta yi sanadin mutuwar yara huɗu tare da jikkata wani yaro guda ɗaya.

Rundunar ’yan sandan jihar, ta tabbatar da aukuwar lamarin a ranar Juma’a.

Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —Gwamnati

Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 12:40 na rana a bayan tashar motar Banki da ke yankin Wajari.

Wani mazaunin garin, Babagana Mohammed, ya kai rahoton fashewar nakiyar da misalin ƙarfe 1 na rana, wanda hakan ya sa aka tura jami’an tsaro zuwa yankin.

DPO na Banki tare da ƙwararrun sashen cire bam, sun killace wajen domin kare jama’a da kuma fara bincike.

An gano cewa wani yaro mai shekaru 12, Mustapha Tijja, ya samu munanan rauni, kuma an kai shi asibitin FHI 360 da ke Banki, inda ake kula da shi.

Rahotanni sun nuna cewa yaron da ya tsira da ransa, yana tare da abokansa huɗu a bayan tashar motar.

Sun samu wani abun fashewa da ake zargin ajiye shi aka yi a wajen, wanda ya fashe yayin da suke wasa da shi.

Yaran da suka rasu sun haɗa da Awana Mustapha mai shekaru 15, Malum Modu mai shekaru 14, Lawan Ibrahim mai shekaru 12 da Modu Abacha mai shekaru 12

Rundunar ’yan sandan jihar, ta ce al’amura sun daidaita a yankin, yayin da a gefe guda ta ke ci gaba da bincike.

Kwamishinan ’yan sandan Jihar, CP Naziru Abdulmajid, ya bayyana alhininsa kan faruwar lamarin, tare da bayyana cewa rundunar tana gudanar da bincike.

Ya gargaɗi jama’a cewa: “A guji taɓa ko wasa da duk wani abu da ba a saba gani ba. Duk abun da ake zargi, a gaggauta sanar da jami’an tsaro.”

Rundunar ta bayyana lambobin kiran gaggawa da jama’a za su yi amfani da su don kai rahoto: 0806 807 5581 da 0802 347 3293.

Kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce rundunar za ta ci gaba da aiki tuƙuru wajen tabbatar da tsaro da hana irin waɗannan abubuwan faruwa a gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • ’Yan bindiga ya hallaka mutum 4, sun sace mata 4 a Sakkwato
  • Nakiya ta hallaka yara 4 a Borno
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026