Aminiya:
2025-12-07@04:29:17 GMT

Jerin ’yan wasan da ke takarar lashe kyautar gwarzon Afirka na bana

Published: 22nd, October 2025 GMT

Hukumar Kula da Harkokin Ƙwallon Ƙafa a nahiyyar Afirka (CAF) ta fitar da sunayen ‘yan takarar da za su lashe kyautar CAF ta shekarar 2025 – rukunin maza.

Cikin wata sanarwa da CAF ta wallafa a shafinta na intanet, ta ce an yi la’akari da rawar da ’yan wasa da masu horarwa suka taka wajen bunƙasa kwallon ƙafa a nahiyar Afirka da ma duniya baki ɗaya.

Hukumar ta ce fitattun masu takarar sun ba da muhimmiyar gudunmawa a fagen tamaula wanda za a yi la’akari da rawar da suka taka a tsakanin ranar 6 ga Janairu zuwa 15 ga Oktoba, 2025.

Idan Tinubu ya gaza zai yi wuya a samu shugaban da zai yi nasara — Shehu Sani Waɗanda ke son rusa Kano ba za su yi nasara ba — Sanusi II

A cikin jerin ’yan wasan nahiyyar Afirka da ke takarar lashe gwarzon shekara na Hukumar CAF akwai sunan ɗan wasan gaban tawagar Super Eagles ta Nijeriya, Victor Osimhen da ɗan wasan gaba na Masar da Liverpool Mohamed Salah, da kuma ɗan wasan baya na Morocco da Paris Saint-Germain, Achraf Hakimi.

Sauran ‘yan takarar sun haɗa da ɗan wasan tsakiya na Kamaru, Frank Anguissa, da Fiston Mayele na Congo, da Denis Bouanga na Gabon, da Serhou Guirassy na Guinea, da Oussama Lamlioui na Morocco, da ‘yan wasan Senegal biyu Iliman Ndiaye da Pape Matar Sarr.

“Tasirin ’yan wasa da masu horar da ‘yan wasa a wasan Afirka da na duniya ya karu sosai a tsawon lokacin da ake yin la’akari da ranar 6 ga Janairu zuwa 15 ga Oktoba 2025, kuma wadannan sunayen nade-nade na nuna wadanda suka ba da babbar gudunmawa ga kwallon kafa a nahiyar,” in ji CAF.

Hukumar ta ce, kwamitin ƙwararru da ya ƙunshi mambobin kwamitin fasaha da ci gaba na CAF, da ƙwararrun koci-koci, CAF Legends da kuma zababbun wakilan kafofin yada labarai, sun yanke shawarar zabar mutane 10 da za a zaba a kowane fanni bisa la’akari da irin rawar da suka taka a dukkan gasa.

Dan wasan Nijeriya, Stanley Nwabali, shi ma an zaɓe shi a matsayin mai tsaron gida na shekara, wanda zai fafata da Yassine Bonou na Morocco, Ronwen Williams na Afirka ta Kudu, Andre Onana na Kamaru, Edouard Mendy na Senegal a takarar mai tsaron gida mafi kyawu na shekara.

Sauran rukunan kyaututtukan sun haɗa da Gwarzon Dan Wasan Interclub, Koci Na Shekara, Gwarzon Matashin Dan Wasan Shekara, Gwarzon Dan Wasan Kasa, da Gwarzon Kulob.

Ga jerin ’yan wasan da ke takarar lashe kyautar gwarzon Afirka na bana:

Andre Frank Zambo-Anguissa (Cameroon/Napoli)
Fiston Mayele (DR Congo/Pyramids)
Mohamed Salah (Egypt/Liverpool)
Denis Bouanga (Gabon/Los Angeles FC)
Serhou Guirassy (Guinea/Borussia Dortmund)
Achraf Hakimi (Morocco/Paris Saint-Germain)
Oussama Lamlioui (Morocco/RS Berkane)
Victor Osimhen (Nigeria/Galatasaray)
Iliman Ndiaye (Senegal/Everton)
Pape Matar Sarr (Senegal/Tottenham Hotspur)

Ga jerin ’yan wasan da ke takarar gwarzon mai tsaron raga:

Andre Onana (Cameroon/Trabzonspor)
Vozinha (Cape Verde/Chaves)
Ahmed El Shenawy (Egypt/Pyramids)
Munir Mohamedi (Morocco/RS Berkane)
Yassine Bonou (Morocco/Al Hilal)
Stanley Nwabali (Nigeria/Chippa United)
Edouard Mendy (Senegal/Al Ahli)
Marc Diouf (Senegal/Tengueth)
Ronwen Williams (South Africa/Mamelodi Sundowns)
Aymen Dahmen (Tunisia/CS Sfaxien)

Ga jerin masu horaswa da ke takarar gwarzon koci na shekara:


Bubista (Cape Verde)
Hossam Hassan (Egypt)
Krunoslav Jurcic (Pyramids)
Sami Trabelsi (Tunisia)
Romuald Rakotondrabe (Madagascar CHAN)
Moine Chaabani (RS Berkane)
Tarik Sektioui (Morocco CHAN)
Mohamed Ouahbi (Morocco U-20)
Walid Regragui (Morocco)
Pape Thiaw (Senegal)

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: da ke takarar la akari da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta gudanar da bikin bude tayin bada kwangilar samar da wutar lantarki a wasu garuruwa dake kananan hukumomin Jihar.

A lokacin da yake jawabi a yayin gudanar da bikin daya gudana a sakatariyar Jihar dake Dutse, Shugaban hukumar, Injiniya Zubairu Musa ya bayyana cewar tayin bada kwangilar samar da wutar da gyara da fadadawa gami da kammala wasu ayyukan za a yi sune a garuruwa 17.

Kazalika, Injiniya Zubairu Musa, yace wannan na daga cikin kudirori 12 na Gwamna Umar Namadi na hada wutar lantarki a kanana da matsakaitan garuruwan jihar da basu da wuta.

A cewar sa, garuruwan da za’a samar da wutar lantarkin a Dutse sun hada da Sabuwar Takur da sabuwar hanyar rukunin gidajen gwamnati na Godiya Miyetti da rukunin gidaje na Bulori da kuma makaranta ta musamman ta Mega.

Shugaban hukumar wanda ya samu wakilcin Sakataren hukumar, Barrista Auwalu Yakubu, yace sauran su ne garin Wurno a karamar hukumar Birnin Kudu da samar da wutar lantarkin a sabbin rukunin gidajen gwamnati na Birnin Kudu da Dutse da Ringim da Babura tare da Kazaure da kuma Gumel.

Sai samar da wutar lantarkin a garin Tsamiyar kwance a karamar hukumar Babura da samar da wutar lantarki a hanyar Nguru da Biranen Hadejia da Kafin Hausa a kananan hukumomin Hadejia da Kafin Hausa.

Ya kara da cewar sai gyara wutar lantarki a garuruwan Addani da Ruruma da Ringim a karamar hukumar Yankwashi da kammala aikin samar da wutar lantarki a garuruwan Tage, Siga, Garin-Wakili, Fandum, Gauta, Ona, Baturiya da Barma-Guwa a karamar hukumar Kirikasamma.

Injiniya Zubairu yace sai kuma samar da wutar lantarki a garin Gwari a Miga da kuma garin Agura a karamar Kafin Hausa.

Sauran sun hada da kammala aikin samar da wutar lantarki a Dandidi a Gagarawa da Matsa a karamar hukumar Malam-Madori da kuma aikin fadada samar da wutar lantarki a Jami’ar Khadija dake garin Majia a karamar hukumar Taura.

A nasa jawabin, wakilin hukumar tantance ayyukan kwangila ta jihar Jigawa, ya ja hankalin ‘yan kwangilar da suka nuna sha’awarsu ta gudanar da aikin da su gudanar da aiki mai inganci, tare da bin dokoki da ka’idojin gudanar da ayyukan kwangila na hukumar.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —Gwamnati
  • Yan Sanda Sun Kama Muhuyi Magaji, Tsohon Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci a Kano
  • Amurka ta Faɗaɗa Jerin ƙasashen Afrika Da ta Sanya wa Takunkumin Visa
  • Mata ‘yar wasan harbi ta Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya a karo na 4
  • Afirka ta Kudu Za Ta Dauki Hutu Daga Halartar Tarukan G20 A Karkashin Shugabancin Trump
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • Dan wasan Taekwando Na kasar Iran Ya Samua Lambar Yabo Ta Zinariya
  • Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa